Connect with us

Fasaha

Zanga-Zanga Saboda Tsadar Rayuwa Ba Mafita Ba Ce — Sarkin Musulmi

Published

on

 

Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya yi kira ga jama’ar Najeriya da su guji gudanar da zanga-zanga domin ba ita ba ce mafita kan halin da ake ciki na tsadar rayuwa a ƙasar.

Kalaman Sarkin Musulmi na zuwa ne yayin jawaban da ya gabatar a fadar gwamnatin Jihar Sakkwato yayin wani taron tattaunawa kan halin da ƙuncin rayuwa da ake fuskanta.

Yayin taron da aka gudanar a wannan makon, Sarkin ya ce tattaunawa kan abin da suka shafe al’umma abu ne mai kyau “domin duk inda mutane suke akwai albarka kasancewarmu ’yan uwan juna.

“Mun sani cewa babu abin da ya buwayi Allah, saboda haka ya kamata a koma a rika addu’a don neman taimakonSa.

“Akwai buƙatar gwamnati ta yi tunani mai kyau don wasu ba haka suke ba suna fita suna gudanar da zanga-zanga wanda hakan ba shi ne mafita ba.

“Dole a taru a gaya wa juna gaskiya shi ne zai fi samar da nasara shugabanni su shawo kan matsalolin da ake ciki.

“Ya kamata mu zauna da shugabannin kungiyoyi mu tattauna su ba mu shawara.

“Kuma bayan zaman neman shawarwari za mu sanar da gwamnati abin da ake ganin ya kamata ta aiwatar don su ne mafita. Gwamnati tana aiki ne domin talaka ba wai talaka ne zai yi wa gwamnati aiki ba.

“Ya zama wajibi a haɗa kai don taimaka wa gwamnati a shawo kan matsalar, musamman rashin tsaro wadda ita ce ta hana mu noma da samun abinci a garuruwanmu .

“Saboda haka a ɗaura ɗamara wajen gudanar da addu’o’i don ganin Allah Ya sawwaka mana matsaloli,” a cewar Sarkin Musulmi.

Kazalika, ya buƙaci shugabanni da a koyaushe a riƙa tunatar da su kan tsoron Allah “domin shugabancin da ya ba mu abin tambaya ne.

“Mun sani cewa gwamnati ta damu da halin da ake ciki kuma da ikon Allah sauki zai samu, saboda haka a ci gaba da haƙuri da yi wa shugabannin addu’a.”

Labarai

Labarai2 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai2 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai2 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi2 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai3 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai3 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai4 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai4 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai4 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai4 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara