Ilimi
Abin Da Ya Sa Ba A Cika Satar Ɗalibai Ba A Borno — Zulum
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya bayyana riko da tsarin nan na “safe school initiative” a matsayin sirrin da ya sa ba cika samun labarin satar ‘yan makaranta ba a jihar.
Tsarin na “safe school initiative” dai wani shiri ne da ya wajabta gina katanga da daukar ma’aikata masu ɗauke da makamai domin kare lafiya da dukiya a makarantu.
Zulum ya bayyana ne Fadar Gwamnatin Najeriya jim kaɗan bayan fitowarsa daga wani taro na shuwagabanni a kasar nan.
Zulum ya ce “Mun kai akalla shekara bakwai zuwa takwas da ƙaddamar da tsarin ‘Safe School Initiative ’ a Jihar Borno.“Kusan duk makarantunmu na da katanga, mun gayyaci sojoji da ’yan sanda aikin tsare ɗalibai da makarantunmu.”
Zulum ya kara da cewa “Mun ɗauki ’yan banga da ’yan sa-kai suna taimaka wa jami’an tsaron kasar nan yadda ya kamata wurin tabbatar da tsaro a makarantun Jihar Borno.”
Gwamna Zulum ya jinjina wa jami’an tsaron bisa ƙoƙarin da ya ce suna yi wurin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a Borno da sauran sassan kasar nan.
Jihar Borno dai ɗaya ce daga cikin jihohin da suka sha fama da bala’in ta’addancin kungiyar Boko Haram da ISIS masu tada ƙayar baya.
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai18 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3