Connect with us

Labarai

An umarci ma’aikatan gwamnati su rinƙa motsa jiki duk mako a Uganda

Published

on

Gwamnatin Uganda ta umarci dukkan ma’aikatanta da su rinƙa ware sa’a biyu a duk mako suna motsa jiki domin su kasance cikin ƙoshin lafiya.

Gwamnatin ta ce an bayar da umarnin ne domin ceton rayukan ma’aikatan da kuma rage musu kamuwa da wasu cutuka da suka jiɓanci rashin motsa jiki.

Cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, gwamnatin ta ce an ɗauki wannan matakin ne domin a canja yanayin tsarin rayuwar ma’aikata da kuma rage haɗarin kamuwa da cutuka a ƙasar.

Gwamnatin ta ɗauki wannan matakin ne bayan wani bincike da hukumar lafiya ta ƙasar ta gudanar wanda ya nuna an samu ƙaruwar masu ƙiba sosai a ƙasar da ya kai daga kashi 17 cikin 100 zuwa 26 cikin 100.

Ba wannan ne karon farko da gwamnatin ta Uganda ta fara bayar da irin wannan umarni ba,ko a 2018 ma an yi wasu abubuwa makamantan haka.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai3 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai3 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai16 hours ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha3 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci3 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi3 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara