Connect with us

Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbe Wani Basarake A Jihar Taraba

Published

on

A safiyar Juma’a 19 ga watan Afrilun 2024, al’ummar masarautar Sansani da ke karamar hukumar Gassol a jihar Taraba suka wayi gari da mummunan labarin kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa Basarake Abdulmutallib Nuhu.

Wannan lamari ya faru ne ‘yan sa’o’i kadan kafin a fara bikin kamun kifi na Nwonyo, wanda ya shafe shekaru 14 ba a yi ba, sai a wannan lokaci da gwamnatin Gwamna Agbu Kefas ta sake farfado da shi.

An shirya gudanar da bikin ne a karamar hukumar Ibi ta jihar, kusa da kogin Benue a kudancin jihar ta Taraba.

Sansani yana da nisan kilomita kaɗan daga karamar hukumar Ibi, wurin da aka keɓe don bikin Kamun Kifin na Nwonyo.

A cewar Danmasanin Sansani, Salihu Sansani, kuma  yayan marigayin, ‘yan bindigar sun isa garin Sansani ne da misalin karfe 9 na daren ranar Alhamis, inda suka doshi fadar kai tsaye suka kashe sarkin.

Ya shaida wa manema labarai cewa maharan sun zo ne a kan babura, inda suka harbe dan uwansa, sannan suka arce da wayoyinsa guda biyu.

A yayin da suke barin kauyen, sun ci karo da wani matashi a kan babur, inda  suka harbe shi a kafa.” in ji Danmasani.

Sai dai wani babban jami’in ‘yan sanda da ke aiki a yankin Sansani ya shaida wa wakilinmu cewa tuni rundunarsa ta fara bibiyar wadanda suka kashe babban basarake.

A lokacin hada wannan rahoto, Mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, ASP James Lashen, ya bayyanawa manema labarai ta wayar tarho cewa yana kan hanyarsa ta zuwa ofishin don sanin halin da ake ciki game da lamarin.

Sani Sulaiman

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai14 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai14 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai1 day ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha4 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci4 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi4 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara