Connect with us

Labarai

‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane A Kwara

Published

on

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kwara ta kama wasu mutane goma sha daya da ake zargi da laifin yin garkuwa da mutane, da kisan kai, da fashi da makami, da mallakar makamai ta haramtacciyar hanya.

Da yake gabatar da wanda ake zargin a hedikwatar ‘yan sanda da ke Ilorin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Victor Olaiya ya ce an kama wadanda ake zargin ne a sassa daban-daban na jihar.

A cewar sa an samu nasarar hakan ne sakamakon  jajircewa, da kuma kwazon jami’an rundunar.

Mista Olaiya  dukkan mutanen su 11 sun amsa laifinsu.

Ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun jagoranci masu bincike zuwa maboyar su inda aka kwato kayayyakin da suka hada da bindigogi da layu.

Kwamishinan ya bayyana cewa za a gurfanar da duk wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Mista Olaiya ya gargadi masu aikata laifuka da su sauya halayensu ko kuma su nisanci jihar.

Ya ce rundunar za ta ci gaba da hada kai da sauran jami’an tsaro domin ganin an dakile aikata laifuka a jihar.

Mista Olaiya ya yi kuma yi kira ga daukacin al’umma da su sanya ido sosai tare da kai rahoton duk wani abin da baake zargi ga hukumomin tsaro domin daukar matakin gaggawa.

Ali Muhammad Rabi’u

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai12 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai12 hours ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai1 day ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai3 days ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha4 days ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci4 days ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi4 days ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai6 days ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi6 days ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai1 week ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Mafi Shahara