Labarai
‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane A Kwara
Rundunar ‘yan sanda a jihar Kwara ta kama wasu mutane goma sha daya da ake zargi da laifin yin garkuwa da mutane, da kisan kai, da fashi da makami, da mallakar makamai ta haramtacciyar hanya.
Da yake gabatar da wanda ake zargin a hedikwatar ‘yan sanda da ke Ilorin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Victor Olaiya ya ce an kama wadanda ake zargin ne a sassa daban-daban na jihar.
A cewar sa an samu nasarar hakan ne sakamakon jajircewa, da kuma kwazon jami’an rundunar.
Mista Olaiya dukkan mutanen su 11 sun amsa laifinsu.
Ya bayyana cewa wadanda ake zargin sun jagoranci masu bincike zuwa maboyar su inda aka kwato kayayyakin da suka hada da bindigogi da layu.
Kwamishinan ya bayyana cewa za a gurfanar da duk wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Mista Olaiya ya gargadi masu aikata laifuka da su sauya halayensu ko kuma su nisanci jihar.
Ya ce rundunar za ta ci gaba da hada kai da sauran jami’an tsaro domin ganin an dakile aikata laifuka a jihar.
Mista Olaiya ya yi kuma yi kira ga daukacin al’umma da su sanya ido sosai tare da kai rahoton duk wani abin da baake zargi ga hukumomin tsaro domin daukar matakin gaggawa.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days ago
Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Fasaha4 days ago
An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar
-
Labarai12 hours ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai1 day ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Kasuwanci4 days ago
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno
-
Ilimi4 days ago
Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert