Labarai
‘Yan Sanda Sun Ceto Dan Kasar Sin Da Aka yi Garkuwa Da Shi A Kwara
Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ceto wani dan kasar Sin wato China ami suna PengChao Zhang da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi a Eiyenkorin da ke karamar hukumar Asa ta jihar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan DSP Ejire-Adeyemi Toun ya fitar, ya ce wasu ‘yan bindiga shidda sun yi garkuwa da Mista PengChao Zhang, wanda aka fi sani da Williams Kaka a lokacin da yake da abokan kasuwancinsa da a wani massukin baki a ranar 10 ga Maris, 2024.
Sanarwar ta ce, rundunar da ‘yan tare da hadin gwiwar jami’an sa kai sun aiwatar da jerin bincike da suka kai ga ceto dan kasarSin din.
Sanarwar ta bayyana cewa, tuni aka sada shi da iyalansa ba tare da wani rauni ba.
Ta kara da cewa, wannan nasara da aka samu na nuna jajircewar rundunar ‘yan sandan jihar wajen tabbatar da tsaro ga dukkan mazauna jihar da maziyartan jihar.
Rundunar ‘yan sandan ta kum bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro domin daukar matakin gaggawa.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai6 days ago
An Kashe Makiyaya 2 Da Shanu 150 A Sabon Hari A Filato