Kasuwanci
Shaguna ‘180’ sun ƙone a gobarar a kasuwar Gandu Sokoto
Wata gobara da ta tashi a babbar kasuwar jihar Sokoto da safiyar yau Litinin ta yi sanadin ƙonewar shaguna da dama a ɓangaren masu sayar da babura da kekuna.
Garba Muhammad Gwazi, shugaban ƴan mashin reshen jihar ya shaida cewa gobarar ta laƙume shaguna ‘180’ na masu sayar da mashin.
A cewarsa, har yanzu ba a san abin da ya janyo tashin gobarar ba da ta janyo asarar dukiya ta miliyoyin naira. Sai dai ya ce gobarar ta soma ne daga wata shara da aka tara.
Ya bayyana cewa gobarar ba ta kai ga asarar rai ko jikkata ba.
Gwazi ya kuma yi kira ga gwamnati ta kai masu ɗauki domin “kasuwancinmu ya miƙe ya ci gaba.” in ji shi.
Shi ma Honarabul Ibrahim Muhammad Giɗaɗo, mai bai wa gwamna shawara kan babbar kasuwar ya ce wutar ta tashi da sanyin safiyar yau.
Ya ce “ɓangaren da ya ƙone sosai a cikin kasuwar shi ne na ƴan mashin da kekuna, ana iya samun shago guda ɗauke da mashin fiye da 200 ko 100, shagunan gaba ɗaya sun ƙone,”
“Waɗannan mashina akwai waɗanda suka haura miliyan, akwai asara mai yawa.” ya ƙara da cewa.
Giɗaɗo ya ƙara da cewa jami’an kashe gobara sun kashe kashi 80 cikin 100 na gobarar da ke ci
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai20 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3