Labarai
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dauki Matakan Kawar Da Nama Me Guba A Kasuwannin Jihar
Gwamnatin jihar Kwara ta ce ta samar da matakan kare lafiyar jama’a a daidai lokacin da ake ta yayata jita-jitar sayar da naman Sa me guba a wasu kasuwannin jihar.
A cikin wata sanarwa da kwamishinar lafiya ta jihar, Dr. Amina Ahmed El-Imam ta fitar, ta ce an kafa wata babbar tawaga don sanya ido kan lamarin.
Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin jihar ta kwace dukkan naman da ake zargi domin yin gwaji akan su, bayan wata ganawa da aka yi da masu ruwa da tsaki naKasuwar.
Sanarwar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, yayin da ake ci gaba da bincike don tabbatar da gaskiyar lamarin.
Sanarwar ta kuma yabawa shugabannin kasuwar bisa hadin kan da suka bayar don shawo kan lamarin.
Sama da shanu talatin da uku 33 ake zargin sun mutu sakamakon guba a yankin Atere da ke Ilọrin.
An kuma yi zargin cewa an yanka matattun dabbobin ne aka raba wa mahauta domin sayarwa a kasuwanni.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai3 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai5 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas