Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dauki Matakan Kawar Da Nama Me Guba A Kasuwannin Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Kwara ta ce ta samar da matakan kare lafiyar jama’a a daidai lokacin da ake ta yayata jita-jitar sayar da naman Sa me guba a wasu kasuwannin jihar.

A cikin wata sanarwa da kwamishinar lafiya ta jihar, Dr. Amina Ahmed El-Imam ta fitar, ta ce an kafa wata babbar tawaga don sanya ido kan lamarin.

Sanarwar ta bayyana cewa, gwamnatin jihar ta kwace dukkan naman da ake zargi domin yin gwaji akan su, bayan wata ganawa da aka yi da masu ruwa da tsaki naKasuwar.

Sanarwar ta bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, yayin da ake ci gaba da bincike don tabbatar da gaskiyar lamarin.

Sanarwar ta kuma yabawa shugabannin kasuwar bisa hadin kan da suka bayar don shawo kan lamarin.

Sama da shanu talatin da uku 33 ake zargin sun mutu sakamakon guba a yankin Atere da ke Ilọrin.

 

An kuma yi zargin cewa an yanka matattun dabbobin ne aka raba wa mahauta domin sayarwa a kasuwanni.

 

Ali Muhammad Rabi’u

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Ilimi3 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai3 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai5 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai5 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Fasaha1 week ago

An Bukaci Gwamnatin Sakkwato Ta Agaji Jami’ar Jihar

Kungiyar Malaman Jami’ar Jihar Sakkwato ASUU-SSU ta yi kira ga gwamnatin Jihar ta duba halin da kungiyar ke ciki da...

Kasuwanci1 week ago

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

  Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin...

Ilimi1 week ago

Zamu Zuba Jarin Dala Miliyan 600 a Nijeriya – Mr. Robert

Shugaba Kasa Bola Tinubu ya samu masu zuba jarin dala miliyan 600 daga kamfanin sufurin jiragen ruwa na kasar Denmark,...

Labarai2 weeks ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Mafi Shahara