Connect with us

Labarai

Kotu Ta Bada Belin Tsohon Gwamnan Jihar Kwara

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke Ilorin babban birnin jihar Kwara, ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar, Alhaji Abdulfatah Ahmed a kan kudi naira miliyan hamsin, bisa zargin almubazzaranci da kudade a lokacin da yake mulki daga shekarar 2011 zuwa 2019.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Abdulfatah bisa zargin almubazzaranci da kudaden jama’a har Naira Miliyan Dubu Daya .

Tsohon gwamnan, wanda ya kai kansa zuwa ofishin hukumar EFCC shiyyar Ilorin a ranar Litinin 19 ga watan Fabrairun 2024, an tsare shi ne bisa wasu sharuddan beli.

A hukuncin da ta yanke bayan sauraron bangarorin biyu, Mai shari’a Evelyn Anyadike ta bayar da sharuddan beli guda takwas domin sakin tsohon gwamnan.

 

Mai shari’a Anyadike ta ce sharuddan belin sun hada da Naira miliyan 50 , da mutum biyu da za su tsaya masa da kadarorinsu a garin Ilorin da kuma mika fasfo dinsa na tafiye-tafiye zuwa kasashen waje ga magatakardar kotun, da dai sauransu.

Da yake amsa tambayoyi daga manema labarai, lauyan hukumar EFCC Rotimi Jacobs (SAN) wanda ya bayyana cewa wanda ake kara yana kan shari’a da tuhume-tuhume 12, ya kuma ki amsa laifinsa a lokacin da aka karanta masa tuhume-tuhumen.

A nasa tsokacin, lauyan wanda ake kara, Kehinde Eleja (SAN), ya koka da yadda ake musgunawa wanda yake karewa.

An dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranakun 29 da 30 ga watan Afrilu na wannan shekara ci gaba da domin sauraren karar

Ali Muhammad Rabi’u

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara