Labarai
Kotu Ta Bada Belin Tsohon Gwamnan Jihar Kwara
Wata babbar kotun tarayya da ke Ilorin babban birnin jihar Kwara, ta bayar da belin tsohon gwamnan jihar, Alhaji Abdulfatah Ahmed a kan kudi naira miliyan hamsin, bisa zargin almubazzaranci da kudade a lokacin da yake mulki daga shekarar 2011 zuwa 2019.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Abdulfatah bisa zargin almubazzaranci da kudaden jama’a har Naira Miliyan Dubu Daya .
Tsohon gwamnan, wanda ya kai kansa zuwa ofishin hukumar EFCC shiyyar Ilorin a ranar Litinin 19 ga watan Fabrairun 2024, an tsare shi ne bisa wasu sharuddan beli.
A hukuncin da ta yanke bayan sauraron bangarorin biyu, Mai shari’a Evelyn Anyadike ta bayar da sharuddan beli guda takwas domin sakin tsohon gwamnan.
Mai shari’a Anyadike ta ce sharuddan belin sun hada da Naira miliyan 50 , da mutum biyu da za su tsaya masa da kadarorinsu a garin Ilorin da kuma mika fasfo dinsa na tafiye-tafiye zuwa kasashen waje ga magatakardar kotun, da dai sauransu.
Da yake amsa tambayoyi daga manema labarai, lauyan hukumar EFCC Rotimi Jacobs (SAN) wanda ya bayyana cewa wanda ake kara yana kan shari’a da tuhume-tuhume 12, ya kuma ki amsa laifinsa a lokacin da aka karanta masa tuhume-tuhumen.
A nasa tsokacin, lauyan wanda ake kara, Kehinde Eleja (SAN), ya koka da yadda ake musgunawa wanda yake karewa.
An dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranakun 29 da 30 ga watan Afrilu na wannan shekara ci gaba da domin sauraren karar
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar