Connect with us

Kasuwanci

Kwastam Ta Fara Rabon Kayan Abincin Da Ta Kwato

Published

on

Hukumar Kwastam ta Kasa, ta fara rabon kayan abincin da ta kwato daga hannun masu fasa kwauri don rage yunwa da tsadar rayuwa da ake fama da su a Najeriya.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da rabon kayan abincin a Legas a ranar Alhamis, Kwanturolan hukumar, Mista Wale Adeniyi, ya ce gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin raba kayan abincin da suka kwato.

 

Ya ce hukumar ta hada kai da wasu hukumomi domin raba kaya abincin ga ’yan Najeriya.

A cewarsa kafin a bai wa mutum kayan abincin, dole ne ya gabatar da lambar shaidar ɗan kasa ta (NIN) don cin gajiyar rabon.

“Za mu hada hannu da masu sana’ar hannu, malamai, kungiyoyin addinai da sauran ‘yan Najeriya a fannin ayyukan kwastam.

“Manufar raba wannan kayan shi ne rage radadin halin da ake ciki a yanzu na yunwa.”

Ya ce matakin na daga cikin kokarin gwamnatin tarayya ke yi na tabbatar da rage farashin kayan abinci da suka yi tashin gwauron zabi a fadin kasar nan.

“Mun hada kai da sauran hukumomin gwamnati, don jagorantar rabon kayan abinci.

Adeniyi, ya ce daga cikin kayan abincin da hukumar za ta raba sun hadar da shinkafa, wake, taliya, macaroni, man gyada, man ja, masara, dawa, da sauran dangin kayan abinci masu yawa.

Wannan na dai na zuwa ne bayan da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayayyaki suka tsefe a kasar.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai18 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai19 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara