Kasuwanci
Kwastam Ta Fara Rabon Kayan Abincin Da Ta Kwato
Hukumar Kwastam ta Kasa, ta fara rabon kayan abincin da ta kwato daga hannun masu fasa kwauri don rage yunwa da tsadar rayuwa da ake fama da su a Najeriya.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da rabon kayan abincin a Legas a ranar Alhamis, Kwanturolan hukumar, Mista Wale Adeniyi, ya ce gwamnatin tarayya ta bayar da umarnin raba kayan abincin da suka kwato.
Ya ce hukumar ta hada kai da wasu hukumomi domin raba kaya abincin ga ’yan Najeriya.
A cewarsa kafin a bai wa mutum kayan abincin, dole ne ya gabatar da lambar shaidar ɗan kasa ta (NIN) don cin gajiyar rabon.
“Za mu hada hannu da masu sana’ar hannu, malamai, kungiyoyin addinai da sauran ‘yan Najeriya a fannin ayyukan kwastam.
“Manufar raba wannan kayan shi ne rage radadin halin da ake ciki a yanzu na yunwa.”
Ya ce matakin na daga cikin kokarin gwamnatin tarayya ke yi na tabbatar da rage farashin kayan abinci da suka yi tashin gwauron zabi a fadin kasar nan.
“Mun hada kai da sauran hukumomin gwamnati, don jagorantar rabon kayan abinci.
Adeniyi, ya ce daga cikin kayan abincin da hukumar za ta raba sun hadar da shinkafa, wake, taliya, macaroni, man gyada, man ja, masara, dawa, da sauran dangin kayan abinci masu yawa.
Wannan na dai na zuwa ne bayan da ‘yan Najeriya ke ci gaba da kokawa kan yadda farashin kayayyaki suka tsefe a kasar.
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai19 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai18 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati