Kasuwanci
Hukumar Kwastam Shiyar Jihar Kebbi Ta Sake Bude Kan Iyakar Najeriya Da Nijar
Sabon Shugaban Hukumar Kwastam a Jihar Kebbi, Kwanturola Iheanacho Ernest Ojike, ya bi umarnin Shugaban Hukumar na kasa Bashir Adewale Adeniyi, na sake bude kan iyakar Kamba don ci gaba da hada-hadar kasuwanci a kasashen duniya.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Mohammed Tajuddeen Salisu ya fitar, ya ce Kamba babbar kan iyaka ce mai matukar mahimmanci, da ke samar da kudaden shiga a jihar Kebbi.
Sanarwar ta bayyana cewa, sake bude kan iyakokin zai kara fadada kasuwanci ta halastacciyar hanya da za su yi tasiri wajen gina kasa da inganta tattalin arziki, yana mai cewa hakan ba ya nufin cewa za a yi sakaci ta yadda wasu za su yi amfani da wannan damar wajen shigo da haramtattun kayayyaki da za su yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da kuma kawo cikas ga tsaron kasa ba.
Kwanturolan na jihar ya ce, jami’an hukumar a shirye suke don yin aiki bisa tsarin doka domin saukaka kasuwanci a kan iyakar Kamba ba tare da wata matsala ba, muddin ‘yan kasuwa sun shigo da halastattun kayayyaki da kuma biyan kudaden da suka dace ga asusun Gwamnatin Tarayya.
Sanarwar ta bayyana cewa, Kwanturola Ernest Ojike yana mai jaddada cewa, har yanzu an haramta fitar da kayan abinci zuwa kasashen waje, bisa la’akari da karancin abinci a kasar.
Abdullahi Tukur
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai16 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3