Connect with us

Labarai

Gidauniyar Aliko Dangote Za Ta Yi Rabon Abinci Na Miliyoyin Naira A Najeriya

Published

on

Shahararran Attajirin nan da ya fi kowa kudi a nahiyar Afirka, Alhaji Aliko Dangote ya kaddamar da rabon abinci kyauta ga al’ummar Musulmi masu azumi su dubu goma a jiharsa ta Kano karkashin gidauniyar Aliko Dangote.

A wata sanarwa da jami’ar gidauniyar a Kano, Samira Sanusi ta fitar, ta ce za kuma a yi rabon buhunan shinkafa har guda miliyan daya da kudinsu ya haura Naira miliyan dubu goma sha uku a fadin jihohi Najeriya 36 da babban birnin tarayya Abuja domin rage radadin halin da yan kasa ke ciki.

Wannan karamci ya biyo bayan rabon biredi dubu ashirin a kullum ga mazauna Kano da kuma dubu goma sha shidda a kullum ga mazauna Legas, da gidauniyar ke yi tun lokacin annobar Korona a shekarar 2020.

Samira Sanusi ta bayyana cewa abincin da za a rika rabawa domin buda baki a wannan watan na Ramadana sun hada da dafadukar shinkafa , da shinkafa da miya , da taliya, da wake tare da kaza da naman Sa, da kuma ruwan sha.

Ta ce ana rarraba abincin ne a masallatan Juma’a, tituna, gidajen yari, da gidajen marayu, da sauran wurare a cikin birnin Kano da kewaye.

Wani wanda ya ci gajiyar abincin mai suna Musa Maikatako mazaunin garin Tarauni ya nuna jin dadinsa da wannan karamcin da ya ce ya taimaka masa wajen yin buda baki cikin sauki.

Maikatako, wanda a bayyane yake cikin farin ciki, ya ce cin abinci kyauta zai taimaka matuka ga wadanda ba sa iya samun abin da za su yi buda baki.

Maikatako ya kuma nuna godiya ga gidauniyar Dangote bisa wannan karimcin, inda ya yi addu’ar Allah Ya kara masa arziki Ya kuma ci gaba da sanya albarka a kasuwancinsa.

Wata wadda ta ci gajiyar tallafin, Hajiya Inna Tukur, ta bayyana jin dadin ta da rabon abincin, wanda a cewarta Gidauniyar Aliko Dangote ta kawo mata dauki.

A cewar ta, ta yi farin ciki da samun abinci mai daɗi kyauta a halin da ake ciki yanzu.

“Ba abin da zan ce sai  godiya gare ku da Aliko Dangote. Ina rokon Allah ya muku albarka,”

Baya ga rabon biredi da aka yi shekara 4 ana yi kyauta, Samira Sanusi ta ce ana ciyar da mabukata a Kano sama da shekaru 30 da suka shude.

A cewarta, ana hakan ne daga gidan mahaifiyarsa da ke Koki da kuma wuraren dafa abinci daban-daban.

“Shirin ciyarwa yana ciyar da mazauna Kano 10,000 a kullum da ya hada da karin kumallo, abincin rana, da kuma abincin dare” in ji ta.

USMAN MZ

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai13 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai13 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci2 days ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha2 days ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha2 days ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai2 days ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi5 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai7 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai7 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara