Labarai
Mutane 10 Sun Mutu A Hadarin Jiragen Soji A Malaysia
Mutane goma ne suka mutu a lokacin da wasu jirage masu saukar ungulu na sojojin Malaysia biyu suka yi karo da juna, yayin wani atisaye da suke yi a yau Talata.
Babban ami’in gudanarwa na hukumar kwana-kwana da aikin ceto ta kasar, Suhaimy Mohamad Suhail ne ya tabbatar da faruwar lamarin.
Firaministan kasar Anwar Ibhrahim ya mika sakon ta’aziyarsa ga iyalan wadanda suka rasu a hadarin da ya bayyana a matsayin mai tada hankali, inda ya ce za a gudanar da bincike don gano musabbabin faruwarsa.
Ba kasafai aka cika samun aukuwar hadarin jiagen sama masu saukar ungulu a kasasshen da ke shiyyar Kudu maso Gabashin nahiyar Asiya ba, amma a watan da ya gabata, wani jirgin sama mai saukar ungulu na jami’an da ke tsaron gabar ruwan Malaysiyan yayi hadari a mashigar Malacca, duk da dai ba a samu asarar rai ba.
Haka nan a shekarar 2016, akwai mataimakin ministan kasar da ya rasu a wani hadarin jirgin sama mai saukar ungulu a jihar Sarawak da ke kasar.
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai3 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Labarai5 days ago
An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas