Connect with us

Labarai

Zanga-Zanga: NLC Ta Damka Wa Majalisa Jerin Bukatun ’Yan Najeriya

Published

on

Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, ya damka wa majalisar dokoki ta kasa kundin bukatun al’ummar Najeriya zuwa ga gwamnatin tarayya.

 

Bukatun da Ajaero ya damka a hannun shugaban Kwamitin Kwadago da Samar da Ayyuka na Majalisar Dattawa, Sanata Diket Plang, sun hada da aiwatar da daukacin bukatun kungiyar kan jin dadin ma’aikata da kuma samar da ayyukan yi ga ’yan kasa.

Sauran su ne, gyara matatun man gwamnati guda hudu da ke kasar da kuma ba wa manoma tallafin noma ba tare da bata lokaci ba, domin saukaka samar da abinci a kasa.

Kwamred Ajaero ya shaida wa Sanata Diket Plang ranar Talata cewa al’ummar Najeriya suna gudanar da zanga-zangar lumanar ce saboda yunwar da ke addabar su, inda ya kwatanta halin da kasar ta tsinci kanta da na kasar Zimbabwe.

Shugaban na NLC ya ce zanga-zangar za ta farkar da gwamnati wajen hanzarta yin abin da ya kamata domin shawo kan matsalolin da ke ci wa kasar tuwo kwarya.

A cewarsa, bangarensu da na gwamnati sun riga sun fara tattaunawa kan batun mafi karancin albashi, amma ba su kai ga cim-ma matsaya ba.

A nasa bangaren, Sanata Plang ya ba su tabbacin tattauna bukatun masu zanga-zangar da nufin ganin an yi abin da ya dace.

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai6 hours ago

Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila

Amurka ta sanar da batun dakatar da shirin ta na kai jirgi dauke da bamabamai zuwa Israila a cikin makon...

Labarai6 hours ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci1 day ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Mafi Shahara