Labarai
Zanga-Zanga: NLC Ta Damka Wa Majalisa Jerin Bukatun ’Yan Najeriya
Shugaban Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), Joe Ajaero, ya damka wa majalisar dokoki ta kasa kundin bukatun al’ummar Najeriya zuwa ga gwamnatin tarayya.
Bukatun da Ajaero ya damka a hannun shugaban Kwamitin Kwadago da Samar da Ayyuka na Majalisar Dattawa, Sanata Diket Plang, sun hada da aiwatar da daukacin bukatun kungiyar kan jin dadin ma’aikata da kuma samar da ayyukan yi ga ’yan kasa.
Sauran su ne, gyara matatun man gwamnati guda hudu da ke kasar da kuma ba wa manoma tallafin noma ba tare da bata lokaci ba, domin saukaka samar da abinci a kasa.
Kwamred Ajaero ya shaida wa Sanata Diket Plang ranar Talata cewa al’ummar Najeriya suna gudanar da zanga-zangar lumanar ce saboda yunwar da ke addabar su, inda ya kwatanta halin da kasar ta tsinci kanta da na kasar Zimbabwe.
Shugaban na NLC ya ce zanga-zangar za ta farkar da gwamnati wajen hanzarta yin abin da ya kamata domin shawo kan matsalolin da ke ci wa kasar tuwo kwarya.
A cewarsa, bangarensu da na gwamnati sun riga sun fara tattaunawa kan batun mafi karancin albashi, amma ba su kai ga cim-ma matsaya ba.
A nasa bangaren, Sanata Plang ya ba su tabbacin tattauna bukatun masu zanga-zangar da nufin ganin an yi abin da ya dace.
-
Labarai6 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai7 days ago
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
-
Labarai6 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi4 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha1 day ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci1 day ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha1 day ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet