Connect with us

Labarai

NLC jihar Plateau ta bi sahun takwarorinta wajen zanga zangar tsadar rayuwa.

Published

on

Shugaban kunguyar a Jihar Plateau Comrade Eugene Manji yace tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasan Nan ya wuce tunanin kowane Dan kasan Nan.

Masu gangamin sunyi kwanba a shataletalen sakatariyar jihar inda suka bayyana irin damuwar da suke cikinta game da wannan tsaadar rayuwa da ta musu dabaibayi.

Shuganan kungiyar a jihar Plateau Comrade Eugene Manji yace cire tallafin Mai ba tare da wani kwakkwaran shiri ba, shi ne ummul’aba’isin fadawa cikin wannan masifar.

Hakama ya bayyana matukar damuwarsu game da canjin kudaden kasashen waje ya kasance.

Comrade Manjin duk da haka Kuma, gwamnati ta kasa cika alkawarinta na samarda motocin safa safa masu amfani da gas da gyaran matatun man fetur, da wutar lantarki da dai sauran matakan rage tsadar rayuwar ga ‘yan Nijeriya.

Ya bayyana matukar damuwarsa ganin cewa duk da tashin gwaron zabin kusan komai a kasan nan, amma albashin da ake biyan ma’aikata bai taka kara ya karya ba.

Sannan ya godewa ‘yan kwadago saboda amsa Kiran da sukayi suka yi fitowar farin dango duk irin matsin rayuwar da ake ciki, tare da shan alwashin kungiyar kwadago zata ci gaba da Kare hakkin ma’aikata da ‘yan Nijeriya ba tare da gajiyawa ba.

Farfesa Kiri Jaryam shi ne yayi magana a madadin kungiyar malaman jami’a ya bukaci dukkannin ‘yan Nijeriya da su hada kansu don a gudu tare a tsira tare.

Dr. Makuyai Godwin yayi magana a madadin kungiyar malaman kwalejojin kimiyya da fasaha da kuma Anthony Joro da ya wakilci kungiyar manyan ma’aikata sun bukaci gwamnati ta tabbatar da ‘yan Nijeriya sun sami saukin rayuwa.

Josiah/Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai5 mins ago

NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo ya karbi tawagar gani da ido...

Kasuwanci24 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai7 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Mafi Shahara