Connect with us

Labarai

’Yar Najeriya Ta Lashe Gasar Alkur’ani Ta Duniya

Published

on

’Yar Najeriya mai shekaru 19 mai suna Hajara Ibrahim Dan’azumi, ta lashe gasar karatun Alkur’ani ta Duniya ta bana.

Malama Hajara ta zama Gwarzuwar Shekara ce bayan da ta samu maki 99.5 a Gasar Hashimite ta Karatun Alkur’ani da Tajwidi ta Mata ta Duniya.

Hajara, wadda ta wakilci Najeriya, a gasar karatun Alkur’ani Izu 60 da Tajwidi, ta yi nasarar doke mahaddata Alkur’ani 40 daga kashe 38 da suka fafata a gasar.

Karo na 18 da aka gudanar da Gasar Karatun Alkur’ani ta Hashemite da gwamnatin kasar Jordan ta gudanar ta kuma karbi masaukin baki.

Malama Hajara dalibar aji biyu ce a Jami’ar Jihar Gombe da kuma Makarantar Islamiyya ta Abubakar Siddiq Islamiyya da ke jihar.

Kafin yanzu, Malama Hajara Dan’azumi ce ta zo ta hudu a rukunin haddar Izu 40 a gasar karatun Alkur’ani ta kasa karo na 34 da aka gudanar a Jihar Legas.

A waccan gasar ta samu maki 97.1 a yayin da kanwarta Maryam ta zo ta daya a rukunin Izu 10 da Tangimi; daya ‘yar uwarta Safiya kuma, ta zo ta 8 a rukunin Izu 40.

Mahaddata 41 daga kasashe 39 ne dai suka fafata a gasar da aka gudanar a kasar Jordan, wadda Hajara ta lashe.

Gwamnan jihar Gombe ya bayyana farin cikinsa tare da alfahari da wannan nasara da matashiyar ta samu a fannin Alkur’ani a duniya.

Ya bayyana jinjinarsa ga malamanta da kuma iyayenta bisa jajircewarsu da ta kai matashiyar ga wannan mataki na daukaka.

Mahaddata 41 daga kasashe 39 ne dai suka fafata a gasar da aka gudanar a kasar Jordan, wadda Hajara ta lashe.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara