Kasuwanci
Gwamnatin Kano Ta Bude Wasu Runbunan Ajiya 10 Da Aka Rufe
Hukumar karɓar ƙorafe-ƙorafen jama’a da yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ta buɗe wasu rumbunan ajiya guda 10 da aka rufe.
Hukumar ta rufe rumbunan ajiyan ne dai a makon da ya gabata bisa zargin ɓoye kayayyakin abinci
Shugaban hukumar Muhyi Magaji, ya bayyana cewa masu rumbunan sun kawo kansu kuma an umarce su da su buɗe su sayar wa jama’a.
Magaji ya ce a dalilin haka jihar Kano ta fara ganin faɗuwar farashin kayan abinci.
“Matakin da hukumar ta ɗauka ya tilasta wa dillalai shigo da kayayyaki kasuwanni tare da rage farashin su, mun kuma ziyarci kasuwanni da dama da suka haɗa da kasuwar hatsi ta Dawanau, kasuwar Singer da kasuwar Kwari da dai sauransu. Idan ka je kasuwar Shuwari a Jigawa da Faskari da sauran kasuwannin jihohi makwabta, za ka ga farashin hatsi ya ragu idan aka kwatanta da baya”.
A cewar Muhuyi, aikin ya yi tasiri sosai wajen rage tashin farashin hatsi da sauran kayayyakin masarufi a jihar.
Ya yi watsi da iƙirarin da shugabannin kasuwar hatsi ta Dawanau suka yi na cewa ba su tara kayan abinci da nufin haifar da ƙarancinsu ba.
-
Fasaha6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Da Kamfanin Sarrafa Sinadarin Batira a Lafiya
-
Ilimi3 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Labarai2 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai6 days ago
Mbappe ya sanar da cewa zai bar PSG a karshen kaka
-
Fasaha3 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai3 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana