Kasuwanci
Hukumar Kwastam Ta Mayar Da Tirela 6 Na Kayan Abinci Da Ta Kwace A Katsina
Hukumar kwastam ta mayar da Tirela shidda na buhunan abinci da ta kama a Kongolam da ke kan iyakar Katsina da Jamhuriyar Nijar a a karamar hukumar Maiaduwa ta jihar Katsina.
Wannan dai ya yi dai-dai da umarnin shugaban kasa kamar yadda shugaban hukumar kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi ya sanar yayin wata ganawa da ya yi da al’ummar yankin iyakar Kongolam a karshen mako.
A lokacin da yake mika motocin guda shida dauke da hatsi a ofishin hukumar kwastam da ke Katsina, shugaban hukumar shiyar Jihar Katsina, Muhammad Umar, ya bayyana cewa an saki buhunan abincin ne ga masu su da sharadin cewa za a sayar da su a kasuwannin Najeriya kawai.
Ya ce jami’an hukumar kwastam sun kwace kayayyakin ne domin aiwatar da dokar hana fitar da kayayyakin abinci da shigo da su daga kasashen waje saboda karancin abinci da hauhawar farashin kayayyaki da ake fuskanta a kasar a halin yanzu.
Kwanturola Umar ya umarci masu wadannan kayayyakin su kasance masu kishin kasa tare da bin ka’idar siyar da kayan abinci a cikin Nijeriya a matsayin hanyar da za ta ci gaba da kokarin tabbatar da wadatar abinci.
Ya kuma kara da cewa, jami’an hukumar tare da hadin gwiwar jami’an Leken asiri da tawagar rundunar hadin gwiwa da ke sintiri a kan iyakokin kasar nan za su sa ido , domin tabbatar da cewa ba a fitar da wadannan kayayyakin daga kasar nan ta barauniyar hanya ba.
Kwanturolan na yankin Katsina ya kuma roki jama’a da su bayar da bayanan da za su taimaka wajen dakile safarar kayayyakin abinci da haramtattun kayayyaki daga kasar nan.
A jawabinsa yayin mika kayayyakin, shugaban kwamitin kula da samar da abinci na jihar Katsina, Jabiru Tsauri, ya gargadi masu safarar kayayyaki da masu motocin da aka sako da su bi umarnin shugaban kasa ta hanyar sayar da hatsin a kasuwannin Najeriya kawai.
Isma’il Adamu
-
Labarai3 days ago
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
-
Kasuwanci4 days ago
CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101
-
Fasaha3 days ago
Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa
-
Labarai5 days ago
An Kwashe Mutane Da Dama Bayan Mummunar Ambaliyar A China
-
Fasaha5 days ago
Mutane 3 Sun Mutu a Salga a Kano
-
Labarai15 hours ago
Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano
-
Labarai5 days ago
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
-
Kasuwanci4 days ago
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Dakatar Da Yanka Nama A Mahauta Na Kwanaki 3