Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kafa Cibiyoyin Bada Abincin Buda Baki A Manyan Makarantu

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kafa cibiyoyin bada abincin buda baki a manyan makarantun jihar guda 10, domin tallafa wa dalibai a lokacin azumi.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai sakamakon taron majalisar zartaswar jihar da aka gudanar a gidan gwamnati na Dutse.

A cewarsa, gwamnatin jihar na shirin ciyar da mutane sama da miliyan uku da dubu dari takwas a watan Ramadan na bana domin tallafawa gajiyayyu da marasa galihu.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya yi nuni da cewa, gwamnatin jihar ta amince da naira kusan miliyan dubu dari uku domin ciyar a watan Ramadan a cibiyoyi 609 da aka kafa a fadin jihar.

Ya ce shirin tallafin da aka tsara ya yi daidai da manufofin gwamnati na rage wahalhalu ga marasa galihu musamman a wannan lokaci na da ake ciki.

Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kafa kwamitin wucin gadi a dukkanin kananan hukumomi 27, wanda kwamishinan kananan hukumomi ko kuma manyan mashawarta na musamman a kananan hukumomin za su jagoranta domin tabbatar da gaskiya.

Sagir Musa ya ce, sauran mambobin kwamitin sun hada da ‘yan majalisar dokokin jihar, mataimaka na musamman, shugabannin kananan hukumomi da DPO na ‘yan sanda.


Sauran sun hada da jami’in tsaro na DSS na karamar hukumar, wakilin hakimai, da sakataren karamar hukuma wanda zai zama sakataren kwamitin.

Hakazalika majalisar ta kuma amince da sama da Naira Biliyan daya da miliyan 125 don ƙarin siyan kayan abinci da za a raba ga marasa galihu, a ƙoƙarin da ake yi na rage wahalhalun rayuwa.

Usman Muhammad Zaria

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Kasuwanci21 hours ago

CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati

Babban Bankin Najeriya CBN ya bayar da wa’adin ranar 7 ga watan  Yulin 2024 ga masu POS su kammala rajista...

Fasaha1 day ago

Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno

  Gwamnatin jihar Borno ta fara aikin horas da malamai 1,949 a matakin farko da aka gano cewa suna iya...

Fasaha1 day ago

Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet

  Babban Bankin Najeriya (CBN) ya umurci bankunan kasar su fara cirar kaso 0.5 cikin 100 na duk kuɗin da...

Labarai1 day ago

An kashe Falasɗinawa 34,800 tun fara yaƙi – Ma’aikatar lafiyar Hamas

Ma’aikatar lafiya ta Hamas a Gaza ta ce an kashe Falasdinawa 34,789 a yankin tun ranar 7 ga watan Oktoba,...

Ilimi4 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin...

Labarai5 days ago

An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya

Shugaban kungiyar masu noman rogo ta Najeriya (NCGA), Mustapha Othman Bakano, ya kaddamar da wani tsari na samar da kasuwa...

Labarai6 days ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu...

Labarai6 days ago

An kama masu zanga-zanga 17 a jami’ar Texas

An sake kama ƙarin mutanen da ke da alaƙa da zanga-zangar nuna goyon baya ga Falasɗinawa inda a wannan karon...

Labarai7 days ago

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah...

Labarai1 week ago

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga...

Mafi Shahara