Connect with us

Labaran Gida

Taiwo Oyedele Zai Maye Gurbin Minista a Ma’aikatar Kudi

Published

on

Daga Bashir Meyere

Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin Mista Taiwo Oyedele a matsayin Ministan kasa,.

Kafin nadin nasa, Mista Taiwo ya kasance Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan dokokin gyaran haraji, inda ya taka rawar gani wajen jagorantar dokokin gyaran haraji da Majalisar Tarayya ta amince da su, sannan Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya rattaba hannu a kansu.

Tabbatar da naɗin nasa ya biyo bayan sa’o’i na tambayoyi masu zurfi daga sanatoci daga jam’iyyun siyasa daban-daban, kan batutuwan tsaro, tattalin arziki da harkokin kuɗi da suka shafi ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin ‘yan Najeriya.

Yayin da yake amsa wasu daga cikin tambayoyin, Taiwo Oyedele ya bayyana cewa sayar da ɗanyen mai na iya taimakawa wajen ƙarfafa tattalin arziki, daidaita kudaden shiga na gwamnati, tare da samar da daidaitaccen farashin man fetur a ƙasar.

Ya ƙara da cewa idan aka kayyade farashi na wani kaso na ɗanyen man Najeriya na wani lokaci, gwamnati za ta iya tabbatar da samun kasafin kuɗi tare da rage tasirin sauyin farashin mai a kasuwannin duniya.

Dangane da matsalar rashin biyan kuɗin ‘yan kwangila saboda ƙarancin kuɗaɗen shiga, Oyedele ya ba da shawarar cewa a rika ba da kwangiloli ne gwargwadon kuɗin da ake da su domin kauce wa taruwar matsalolin biyan kuɗin da sauransu.

Ya bayyana cewa irin wannan yanayi na iya sa kwangilar da aka fara da farashin naira biliyan ɗaya ta tashi zuwa naira biliyan biyu, domin rufe asarar da ‘yan kwangila ke yi sakamakon jinkirin biyan su daga gwamnati.

Game da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga na ƙasar, Oyedele ya ce an fi mayar da hankali kan harajin man fetur da iskar gas, yayin da sauran fannoni kamar ma’adinai ke da babbar dama ta samar da kuɗaɗen shiga, amma ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba.

Oyedele ya jaddada buƙatar yin sahihin kasafin kuɗi  tare da aiwatar da ayyukan da aka amince da su yadda ya kamata. Ya ce idan aka yi kasafin kuɗi, dole ne a tabbatar da cewa akwai kuɗin da za a aiwatar da shi, tare da sakin kuɗaɗe domin a kammala ayyukan musamman na ababen more rayuwa.

A jawabin sa bayan tabbatar da naɗi, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya yabawa Shugaba Bola Tinubu kan naɗin Oyedele, yana mai cewa mutum ne mai ƙwarewa kuma ya dace da wannan muƙami.

Labarai

Labarai20 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai21 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai21 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara