Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta Amince da Kudirin Kasafin 2026

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta amince da Kudirin Dokar Kasafin Kuɗin shekarar 2026 na sama da naira biliyan 901, tare da sanya hannu ya zama doka, bayan yin wasu gyare-gyare.

Wannan ya biyo bayan gabatarwa da kuma amincewa da rahoton Kwamitin Majalisar kan Kasafin Kuɗi.

Yayin gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin wanda ke wakiltar Mazabar Malam Madori, Alhaji Hamza Adamu Ibrahim, ya bayyana cewa dukkan Kwamitocin Majalisar sun tattauna da Ma’aikatun Gwamnati da Hukumominsu kan tantancewa da kare ƙididdigar kasafin kuɗinsu.

Ya ce duba da abubuwan da kasafin ya ƙunsa, kwamitin ya gamsu da rabon kuɗaɗen da aka ware domin samar da ababen more rayuwa da walwalar al’umma a shekarar kasafin kuɗin 2026.

Dangane da kasafin kuɗin ƙananan hukumomi 27 da ya haura naira biliyan 288, Hamza Adamu ya yi kira ga Ma’aikatar Kananan Hukumomi da ta tabbatar cewa shugabannin ƙananan hukumomi suna bin aiwatar da kasafin kuɗinsu yadda ya dace domin jin daɗin al’ummar karkara.

A yayin zaman Kwamitin Majalisa gaba ɗaya (Committee of the Whole), Shugaban Majalisar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin, ya karɓa tare da duba shawarwari da gyare-gyare kan kura-kurai na rubutu musamman sunayen garuruwa da wurare.

Da aka koma zaman Majalisa na gaba ɗaya, Mataimakin Magatakardar Majalisa, Alhaji Yusha’u Muhammad, ya karanta kudirin dokar karo na biyu da na uku, inda Shugaban Majalisar, Haruna Aliyu Dangyatin, ya sanar da amincewa da Kudirin Dokar Kasafin Kuɗin shekarar 2026 ya zama doka.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara