Connect with us

Ilimi

Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar bunkasa ilimin manya ta jihar Jigawa tace za ta kashe naira milyan 400 wajen gudanar da harkokin ta a sabuwar shekara ta 2026.

Shugaban hukumar. Dr. Abbas Abubakar Abbas, ya bayyana haka lokacin kare kiyasin kasafin kudin hukumar a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Dr Abbas Abubakar Abbas ya ce hukumar za ta yi amfani da kudaden wajen inganta shirye shiryen koyon karatu da rubutu ga manya maza da mata da na ci gaba da karatu don kammala karatun sakandare da na masu son sake jarrabawar sakandire da koyon karatu ta Rediyo da cibiyoyi daban daban da ke fadin jihar.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumarsa , shugaban hukumar makarantun Tsangaya, Dr. Hamisu Maje, ya ce sun yi kiyasin naira milyan dubu 3 da milyan 500 tare da kudurin kammala aikin ginin makarantun Tsangaya guda 3 da ke Ringim da Kafin Hausa da Dutse.

Ya ce an yi tanadi domin kafa cibiyar koyar da sana’oi da gidajen alarammomi da masallaci tare da samar da ruwan sha da wutar lantarki a kowacce makaranta.

Dr. Hamisu Maje ya kuma bayyana cewar hukumar za ta gyara makarantun Tsangaya guda 7 da aka gada daga gwamnatin tarayya da ke sashen jihar domin karfafa tsarin ilimin makarantun Tsangaya na zamani.

A daya bangaren kuma, kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse da Kuma hukumar bada tallafin karatu ta jihar sun kare kiyasin kasafin kudadensu a gaban kwamatin kula da manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Da ya ke kare kiyasin kasafin kudin, shugaban kwalejin fasaha ta jihar da ke Dutse, Dr. Ahmad Badayi, ya ce sun yi kiyasin fiye da naira milyan 700 wadda daga ciki an kebe naira milyan 330 domin sayo kayayyakin aiki a dakin gwaje-gwaje da koyon aikin hannu da gyaran ofisoshi, yayin da za a yi amfani da ragowar kudaden wajen kammala manyan ayyuka.

Shi ma da ya ke kare kiyasin kasafin kudin hukumar sa, shugaban hukumar bada tallafin karatu ta jihar Malam Sa’idu Magaji, ya ce sun yi kiyasin kashe naira milyan dubu 10 domin bada tallafin karatu na cikin gida da na kasashen waje.

A nasa jawabin, shugaban kwamatin kula da ilimin manyan makarantu na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Sule Tankarkar Alhaji Muhammad Abubakar Sa’id, ya jaddada bukatar ganin masu ruwa da tsaki a bangaren manyan makarantu sun yi dukkan mai yiwuwa domin inganta harkokin ilimi mai zurfi a sabuwar shekara.

 

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara