Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta Shiga Jimami Sakamakon Rasuwar ‘Yan Majalisar 2 a Awa Guda

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta shiga jimami mai tsanani sakamakon rasuwar ’yan majalisar su biyu Honarabul Sarki Aliyu Daneji da Honarabul Aminu Sa’adu Ungogo, waɗanda suka rasu a ranar Laraba, da tazarar awa ɗaya kacal.

An ruwaito cewa Honarabul Daneji, wanda ke wakiltar Mazabar Kano Municipal a Majalisar Dokokin Jihar Kano, ya rasu ne kimanin awa ɗaya bayan rasuwar abokin aikinsa, Honarabul Aminu Sa’adu Ungogo.

Darakta Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, Sanusi Dawakin Tofa ne ya tabbatar da rasuwar Daneji cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba.

Tun da farko dai, Majalisar ta yi babban rashi na Aminu Sa’adu Ungogo, ɗan majalisar da ke wakiltar Mazabar Ƙaramar Hukumar Ungogo kuma Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar.

Ungogo, mamba ne na jam’iyyar NNPP kuma rahotanni sun nuna cewa ya rasu ne bayan gajeriyar jinya.

Majiyoyi daga cikin Majalisar sun bayyana cewa marigayi  Ungogo ya halarci Majalisar Dokokin Jihar Kano a ranar da ya rasu, inda ya shiga taron kwamitinsa, lamarin da ya ƙara girgiza abokan aikinsa da ma’aikatan Majalisar.

Rasuwar ’yan majalisar biyu a kusan lokaci guda ta jefa Majalisar cikin alhini tare da girgiza harkokin siyasa a faɗin Jihar Kano.

’Yan majalisa, shugabannin jam’iyyu, jami’an gwamnati da al’ummar mazabunsu na ci gaba da bayyana alhini da kaɗuwa kan wannan lamari, suna bayyana rasuwar a matsayin babban koma baya ga ayyukan Majalisar Dokokin jihar.

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara