Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Shekarar 2026

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya rattaba hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2026 na Naira biliyan 901 da miliyan 804, domin inganta ci gaban jihar tare da biyan buƙatun al’ummar Jigawa.

Da yake jawabi bayan sanya hannu kan kasafin, Gwamna Namadi ya bayyana cewa duk da kasafin jihar ya kai sama da Naira Biliyan, kasafin kuɗin haɗin gwiwa na ƙananan hukumomi 27 ya kai Naira Biliyan 288 da Miliyan 805.

Wannan kasafi sakamakon shirin tattaunawa da al’umma ne da muka gudanar, kuma yana nuna ainihin muradu da burin mutanen Jihar Jigawa.

Saboda haka, kasafin al’umma ne, daidai yadda jama’a suka buƙata, kuma daidai abin da ke ƙunshe a cikin wannan kasafi,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa bisa jajircewa da sadaukarwar da suka nuna a duk tsawon aikin kasafin kuɗin.

Goyon bayansu a yayin tarukan tattaunawa da al’umma, ganawar bangarori biyu, tattaunawa ta manyan shugabanni, da kuma matakan kwamitoci, ya taka muhimmiyar rawa wajen amincewa da wannan kasafi cikin nasara,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar bisa amincewa da kuma shiga  shirin tattaunawa da al’umma, tare tattara ra’ayoyin jama’a, inda da dama daga cikinsu ke aiki har cikin dare.

Haka nan, Namadi ya yaba wa al’ummar jihar bisa goyon baya da kuma halartar su a tsarin kasafin kuɗin, inda ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta yi iya ƙoƙarinta wajen inganta rayuwar al’ummar Jigawa.

 

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara