Labarai
Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL
Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin amfani da naira tiriliyan 210 a kamfanin.
Shugaban kwamitin, Sanata Ahmad Aliyu Wadada, ya bayar da wannan umarni ne bisa ikon da Kundin Tsarin Mulki da dokokin majalisa suka ba shi na kiran kowanne shugaban hukumar gwamnati domin bayyana duk wata mu’amalar kudi.
Sanata Wadada ya ce binciken majalisa ya samo asali ne daga abubuwan da kwamitin ya lura da su a cikin sarrafa kudade yayin duba rahoton babban mai binciken kudi na tarayya na shekarun 2019 da 2020.
Ya ce tun daga lokacin, kwamitin yana binciken bayanan kudade na NNPCL daga shekarar 2017 zuwa 2023, kuma binciken bai tsaya ba saboda an watsar da shi, sai dai saboda suna son yin cikakken bincike domin kada sakamakon ya kasance ba a fahimta ba.
Shugaban kwamitin ya kara da cewa, domin gudanar da wannan aiki yadda ya kamata, kwamitin ya nemi bayanan da suka dace daga NNPCL, kuma kamfanin ya bayar da su.
Kwamitin ya duba bayanan kudade da aka bincika na NNPCL daga 2017 zuwa 2023, wanda masu bincike na waje suka shirya, amma kwamitin bai gamsu gaba daya ba.
Kwamitin ya tabbatar da cewa zai ci gaba da huldar da duk masu ruwa da tsaki wajen gudanar da ayyukansa na majalisa da kuma tsaftace sashen mai da masana’antar man fetur domin ci gaban tattalin arzikin Najeriya.
Cov/ Bashir M
-
Labarai6 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai3 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai4 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai6 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai5 days agoGwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri
-
Labarai2 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
