Connect with us

Labarai

Hakkoki Da Tsare Sirrin Bayanan Maras Lafiya

Published

on

 

A yau za mu duba wani batu na dokoki wadanda musamman mu ma’aikatan lafiya muke takewa na rashin ba da hakkoki da yada sirrin marasa lafiya ga jama’a, a wasu lokuta ma har ga gidajen watsa labarai ba tare da yardarsu ko amincewarsu ba.

Mu ma muna da namu hakkokin a kan marasa lafiya wadanda za a yi maganarsu a mako mai zuwa.

Hakkin marasa lafiya ne mu tsare musu sirrinsu. Tsare sirrin bayanan maras lafiya wajibi ne ga kowane ma’aikacin lafiya.

Akwai dokoki da hukunce-hukunce masu tsauri idan aka samu wani ma’aikacin lafiya da keta haddin bayanan maras lafiya.

Ban da bayanan rashin lafiya, tsare sirrin bayanan maras lafiya ya shafi har da wasu bayanai masu nuni da ko shi wane ne, kamar lambar katin dan kasa ko shekaru ko adireshi da lambobin waya.

Maras lafiya na da hakkin ya kai duk wanda ya keta dokar tsare sirrinsa ga hukuma domin a ba shi hakkinsa.

Dole a fayyace wa maras lafiya dukkan bayanan da yake bukata a game da rashin lafiyarsa, sabanin yadda akan yi biris da marasa lafiya idan sun yi tambaya.

Kuma ba za a ba kowa bayanan maras lafiya ba komai kusancinsu da maras lafiyan, sai da izinin maras lafiya.

Ba za a ba wa kowane ma’aikaci a asibiti wasu bayanai na maras lafiya ba, sai mai lura da shi kai tsaye, kamar likitoci da nas-nas da ke kula da shi.

Idan aka ga wani ma’aikaci yana keta wadannan dokoki dole ne shi ma a kai shi ga hukumomin asibiti domin daukar mataki.

Wadannan dokoki sun shafi kowane ma’aikaci a asibitin tun daga kan shugaba har zuwa masu shara da masu gadi.

Maras lafiya kuma yana da zabi a kan wanda yake so ya kula da shi.

Yana iya tambayar sunansa ko sunanta a fada masa Maras lafiya yana da damar canzawa ko kara neman shawarar wani ma’aikacin lafiyar idan yana son bayanai gamsassu.

Kada a sa mara lafiya cikin binciken aikin lafiya ba tare da sanin sa ba. Idan ma ya ba da goyon baya yana da damar ya fita a duk lokacin da yake so.

Maras lafiya yana da damar a duba shi, a ba shi magani a ko’ina a kasar nan ko ma a ko’ina a duniya ba tare da wani bambancin launin fata ko yare ko addini ko jinsi ba.

Iyaye suna da damar su san ko me ake yi wa ‘ya’yansu na magani idan suka kawo su asibiti ko wane magani ko aiki za a musu. Haka kuma suna da ta cewa a kan magungunan da ake ba yaran.

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara