Labarai
FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara
Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da Al’adu na Zamfara.
Farfesa Adamu ya yi wannan bayani ne yayin da yake jagorantar Majalisar gudanarwa ta jami’ar a ziyara ta girmamawa ga Mai Martaba Sarkin Anka kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara, Alhaji Attahiru Muhammad Ahmad.
Sanarwa daga Babban Sakataren Bayani da Harkokin Jama’a na Jami’ar, Jamilu Ibrahim Gusau, ta bayyana cewa ziyara ta kasance wani bangare ne na huldar da Farfesa Adamu ke yi da masu ruwa da tsaki, yayin da yake tsara manufar gudanarwar sa.
Shugaban jami’ar ya tabbatar cewa gudanarwar sa za ta yi aiki kafada da kafada da Majalisar Sarakunan Jihar Zamfara, domin tabbatar da cewa al’ummar jihar za su amfana daga damar ilimi da ci gaban da FUGUS ke bayarwa.
A jawabin sa, Emir na Anka, Alhaji Attahiru Ahmad, ya yaba wa Shugaban jami’a da ƙungiyar gudanarwa, ya bayyana ziyara a matsayin farkon sabuwar haɗin gwiwa tsakanin jami’a da hukuma ta gargajiya.
Ya nuna cewa ingantaccen haɗin kai zai taimaka sosai wajen magance matsalolin zamantakewa da ci gaba a jihar.
Sarkin ya kuma bayyana cewa Majalisar Sarakuna za ta yi aiki tare da jami’a wajen shirya taruka da bita ga sarakuna, da kuma daidaita rawar da nauyin shugabanci tsakanin masu mukami a fadin jihar Zamfara.
REL/ AMINU DALHATU
-
Labarai6 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai3 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai4 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai6 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai5 days agoGwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri
-
Labarai2 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
