Labarai
Babu Gaskiya A Zargin PDP – Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi
Mataimakin gwamnan jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, ya karyata rade-radin da jam’iyyar PDP ta yi na kin mika mulki daga hannun gwamna a duk lokacin da zai fita daga jihar.
Da yake jawabi a taron manema labarai a Birnin-kebbi, Mataimakin Gwamnan ya ce, sanarwar da ‘yan adawar suka fitar kan ba a bashi iko tafiyar da gwamnati ba wani abu bane illa dai jam’iyyar PDP na kokarin haifar da matsala a inda babu ita.
Sanata Umar Tafida, ya bayyana cewa, daga ranar aka rantsar da wannan gwamnati babu wata rana daya da aka sami gibin shugabanci ko da na yini guda, yana mai cewa, a duk lokacin da Gwamna ba ya jihar Kebbi ko kuma kasar nan domin gudanar da ayyukan gwamnati, yakan ba da amanarsa. ayyuka na yau da kullun da gudanar da ayyukan Jiha ga Mataimakin Gwamna kamar yadda doka ta tanada.
Ya bayyana cewa, akwai kyakkyawar fahimta da kyakkyawar alakar aiki tsakanin Gwamnan da shi kansa a matsayin Mataimakinsa.
Sanata Tafida, ya ce Gwamna da Mataimakin Gwamna da ‘Yan Majalisar Zartaswa duk sun hada kai kuma sun himmatu wajen ciyar da Jihar gaba domin ci gaban al’ummar Jihar Kebbi.
Abdullahi Tukur/Hamisu/Wababe
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
