Labaran Gida
Taiwo Oyedele Zai Maye Gurbin Minista a Ma’aikatar Kudi
Daga Bashir Meyere
Majalisar Dattawa ta tabbatar da naɗin Mista Taiwo Oyedele a matsayin Ministan kasa,.
Kafin nadin nasa, Mista Taiwo ya kasance Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan dokokin gyaran haraji, inda ya taka rawar gani wajen jagorantar dokokin gyaran haraji da Majalisar Tarayya ta amince da su, sannan Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya rattaba hannu a kansu.
Tabbatar da naɗin nasa ya biyo bayan sa’o’i na tambayoyi masu zurfi daga sanatoci daga jam’iyyun siyasa daban-daban, kan batutuwan tsaro, tattalin arziki da harkokin kuɗi da suka shafi ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin ‘yan Najeriya.
Yayin da yake amsa wasu daga cikin tambayoyin, Taiwo Oyedele ya bayyana cewa sayar da ɗanyen mai na iya taimakawa wajen ƙarfafa tattalin arziki, daidaita kudaden shiga na gwamnati, tare da samar da daidaitaccen farashin man fetur a ƙasar.
Ya ƙara da cewa idan aka kayyade farashi na wani kaso na ɗanyen man Najeriya na wani lokaci, gwamnati za ta iya tabbatar da samun kasafin kuɗi tare da rage tasirin sauyin farashin mai a kasuwannin duniya.
Dangane da matsalar rashin biyan kuɗin ‘yan kwangila saboda ƙarancin kuɗaɗen shiga, Oyedele ya ba da shawarar cewa a rika ba da kwangiloli ne gwargwadon kuɗin da ake da su domin kauce wa taruwar matsalolin biyan kuɗin da sauransu.
Ya bayyana cewa irin wannan yanayi na iya sa kwangilar da aka fara da farashin naira biliyan ɗaya ta tashi zuwa naira biliyan biyu, domin rufe asarar da ‘yan kwangila ke yi sakamakon jinkirin biyan su daga gwamnati.
Game da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga na ƙasar, Oyedele ya ce an fi mayar da hankali kan harajin man fetur da iskar gas, yayin da sauran fannoni kamar ma’adinai ke da babbar dama ta samar da kuɗaɗen shiga, amma ba a ba su kulawa yadda ya kamata ba.
Oyedele ya jaddada buƙatar yin sahihin kasafin kuɗi tare da aiwatar da ayyukan da aka amince da su yadda ya kamata. Ya ce idan aka yi kasafin kuɗi, dole ne a tabbatar da cewa akwai kuɗin da za a aiwatar da shi, tare da sakin kuɗaɗe domin a kammala ayyukan musamman na ababen more rayuwa.
A jawabin sa bayan tabbatar da naɗi, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio ya yabawa Shugaba Bola Tinubu kan naɗin Oyedele, yana mai cewa mutum ne mai ƙwarewa kuma ya dace da wannan muƙami.
-
Labarai6 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai6 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai3 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai7 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai5 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
-
Labarai6 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoRamadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji
