Connect with us

Labarai

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Published

on

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin amfani da naira tiriliyan 210 a kamfanin.

Shugaban kwamitin, Sanata Ahmad Aliyu Wadada, ya bayar da wannan umarni ne bisa ikon da Kundin Tsarin Mulki da dokokin majalisa suka ba shi na kiran kowanne shugaban hukumar gwamnati domin bayyana duk wata mu’amalar kudi.

Sanata Wadada ya ce binciken majalisa ya samo asali ne daga abubuwan da kwamitin ya lura da su a cikin sarrafa kudade yayin duba rahoton babban mai binciken kudi na tarayya na shekarun 2019 da 2020.

Ya ce tun daga lokacin, kwamitin yana binciken bayanan kudade na NNPCL daga shekarar 2017 zuwa 2023, kuma binciken bai tsaya ba saboda an watsar da shi, sai dai saboda suna son yin cikakken bincike domin kada sakamakon ya kasance ba a fahimta ba.

Shugaban kwamitin ya kara da cewa, domin gudanar da wannan aiki yadda ya kamata, kwamitin ya nemi bayanan da suka dace daga NNPCL, kuma kamfanin ya bayar da su.

Kwamitin ya duba bayanan kudade da aka bincika na NNPCL daga 2017 zuwa 2023, wanda masu bincike na waje suka shirya, amma kwamitin bai gamsu gaba daya ba.

Kwamitin ya tabbatar da cewa zai ci gaba da huldar da duk masu ruwa da tsaki wajen gudanar da ayyukansa na majalisa da kuma tsaftace sashen mai da masana’antar man fetur domin ci gaban tattalin arzikin Najeriya.

Cov/ Bashir M

Labarai

Labarai4 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai4 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai11 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai11 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai11 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai11 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai11 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai11 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai11 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai11 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara