Connect with us

Labarai

‘Yan Sanda Sun Ceto Yara Mata 28 Da Aka Sace A Katsina

Published

on

Rundunar ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro sun ceto ‘yan matan nan  28 da aka sace daga kauyen Kasai da ke karamar hukumar Batsari a jihar Katsina.

A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Sadiq ya sanya wa hannu, ta ce an kubutar da dukkan ‘yan matan ba tare da wani rauni ba.

‘Yan fashin sun yi wa yaran ‘yan shekara takwas zuwa sha biyar kwanton bauna ne a bayan gari, inda suka je dibar itacen da za su kai gida domin yin girki.

Sanarwar ta ce da samun rahoton faruwar lamarin, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Abubakar, ya tura jami’ai zuwa dajin tare da yin tattaki domin ceto yaran.

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun yi watsi da yaran ne sakamakon matsin lamba da ‘yan sanda suka yi musu, inda suka gudu suka bar  yaran wadanda a halin yanzu suke cikin koshin lafiya.

Kokarin hadin gwiwa da tawagar ceto ta sa kai, tare da dabarun da rundunar ta dauka, ya sa aka sako dukkan wadanda aka sace”. Inji shi.

“Wannan nasara ta nuna jajircewar rundunar da kuma duk wanda ke da hannu acaiki.n ceton.

Sanarwar ta kara da cewa “Za a ci gaba da kokarin tabbatar da  tsaron al’umma da jihar baki daya.

 

Ismai’l Adamu

Labarai

Labarai20 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi20 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai20 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara