Ilimi
Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba
Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin aikin da suke gudanarwa, domin bai wa tattaunawa damar ci gaba don warware matsalolin da ke haddasa rikicin cikin gaggawa.
Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mista Peter Ahemba, ne ya yi wannan roko yayin da yake jawabi ga ’yan jarida a taron manema labarai na watanni biyu-biyu da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.
Mista Ahemba ya ce yajin aikin da Malaman Kwalejin Ilimi ta Akwanga da kwalejin kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai Lafia, da Kwalejin Aikin Noma, Kimiyya da Fasaha ta Lafia ke yi na iya kawo cikas ga karatun dalibai. Saboda haka, ya roki ƙungiyoyin malaman da su koma teburin tattaunawa domin cimma matsaya cikin lumana.
Ƙungiyoyin Malaman Manyan Makarantu na Jihar Nasarawa sun ayyana yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar 29 ga Disamba, 2025, bisa rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa ga mambobinsu.
Babban Mataimakin na Musamman ya bayyana cewa kwanan nan Gwamna Abdullahi Sule ya raba katifa dubu ɗaya da gadaje ga daliban Kwalejin Ilimi ta Akwanga (COEA), domin inganta muhallin koyo da koyarwa.
Ya ce wannan rabon na daga cikin kulawar da gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule ke bai wa fannin ilimi tun daga lokacin da ta hau mulki a shekarar 2019.
Mista Ahemba ya ƙara da cewa gwamnatin ta gina azuzuwa da dama, ta gyara makarantu masu yawa, tare da gina katangar kariya a makarantu da dama domin kare su daga mamaya.
Ya kuma ce gwamnatin ta fahimci yadda wasu miyagun mutane ke shiga jihar a hankali, lamarin da ke barazana ga tsaron mazauna yankin.
Mista Ahemba ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin tsakar dare da wasu da ba a tantance su ba suka kai wa mazauna Akunza da ke yankin Ashige a karamar hukumar Lafia.
Ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnati na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki wajen aiwatar da sabbin matakan tsaro domin shawo kan irin waɗannan hare-hare.
Ya kuma yi kira ga ’yan ƙasa da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen kama masu aikata laifuka a dukkan sassan jihar.
Mista Ahemba ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Saboda haka, ya roki jama’a da su rika kai rahoton duk wani abu da suke zargin ba daidai ba ga hukumomin da suka dace, tare da ba da cikakken haɗin kai ga jami’an tsaro domin hana aikata laifuka da yaki da su.
COV: Aliyu Muraki / Lafia
-
Labarai6 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai3 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai4 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai6 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai5 days agoGwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri
-
Labarai2 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
