Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Nasarawa Ta Roki Malaman Jami’o’i Masu Yajin Aiki Su Koma Aji – SSA Ahemba

Published

on

Gwamnatin Jihar Nasarawa ta yi kira ga malaman manyan makarantu mallakar jihar da ke yajin aiki da su janye yajin aikin da suke gudanarwa, domin bai wa tattaunawa damar ci gaba don warware matsalolin da ke haddasa rikicin cikin gaggawa.

Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mista Peter Ahemba, ne ya yi wannan roko yayin da yake jawabi ga ’yan jarida a taron manema labarai na watanni biyu-biyu da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Mista Ahemba ya ce yajin aikin da Malaman Kwalejin Ilimi ta Akwanga da kwalejin kimiyya da fasaha ta Isa Mustapha Agwai Lafia, da Kwalejin Aikin Noma, Kimiyya da Fasaha ta Lafia ke yi na iya kawo cikas ga karatun dalibai. Saboda haka, ya roki ƙungiyoyin malaman da su koma teburin tattaunawa domin cimma matsaya cikin lumana.

Ƙungiyoyin Malaman Manyan Makarantu na Jihar Nasarawa sun ayyana yajin aikin sai baba-ta-gani a ranar 29 ga Disamba, 2025, bisa rashin aiwatar da sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa ga mambobinsu.

Babban Mataimakin na Musamman ya bayyana cewa kwanan nan Gwamna Abdullahi Sule ya raba katifa dubu ɗaya da gadaje ga daliban Kwalejin Ilimi ta Akwanga (COEA), domin inganta muhallin koyo da koyarwa.

Ya ce wannan rabon na daga cikin kulawar da gwamnatin Gwamna Abdullahi Sule ke bai wa fannin ilimi tun daga lokacin da ta hau mulki a shekarar 2019.

Mista Ahemba ya ƙara da cewa gwamnatin ta gina azuzuwa da dama, ta gyara makarantu masu yawa, tare da gina katangar kariya a makarantu da dama domin kare su daga mamaya.

Ya kuma ce gwamnatin ta fahimci yadda wasu miyagun mutane ke shiga jihar a hankali, lamarin da ke barazana ga tsaron mazauna yankin.

Mista Ahemba ya yi Allah-wadai da kakkausar murya kan harin tsakar dare da wasu da ba a tantance su ba suka kai wa mazauna Akunza da ke yankin Ashige a karamar hukumar Lafia.

Ya tabbatar wa al’umma cewa gwamnati na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki wajen aiwatar da sabbin matakan tsaro domin shawo kan irin waɗannan hare-hare.

Ya kuma yi kira ga ’yan ƙasa da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai da za su taimaka wajen kama masu aikata laifuka a dukkan sassan jihar.

Mista Ahemba ya tabbatar wa jama’a cewa gwamnati na yin duk mai yiwuwa domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Saboda haka, ya roki jama’a da su rika kai rahoton duk wani abu da suke zargin ba daidai ba ga hukumomin da suka dace, tare da ba da cikakken haɗin kai ga jami’an tsaro domin hana aikata laifuka da yaki da su.

COV: Aliyu Muraki / Lafia

Labarai

Labarai38 minutes ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai56 minutes ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai7 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai7 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai7 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai7 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai7 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai7 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai7 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai7 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara