Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin 2026 a Gaban Majalisa

Published

on

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da kasafin kuɗin shekarar 2026 da ya kai Naira Tiriliyan 58.18 ga zaman haɗin gwiwa na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, inda ya bayyana shi a matsayin “Kasafin Ƙarfafa Ci gaba, Sabunta Juriya da Wadata ga Kowa.”

Da yake jawabi ga ’yan majalisa a Abuja, Shugaban ya ce Dokar Kasafin Kuɗi ta 2026 ta ginu ne bisa sauye-sauyen tattalin arziki da aka aiwatar cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata, waɗanda suka mayar da hankali kan daidaita tattalin arziƙin ƙasa, karfafa masu zuba jari, da shimfiɗa tubalin ci gaba mai amfani ga kowa.

Shugaba Tinubu ya tsara kashe naira tiriliyan 15.25 domin gudanar ayyukan yau da kullum na gwamnati, sannan ya ware naira tiriliyan 26.08 domin gudanar da manyan ayyuka da more rayuwa a ƙasar.

Tinubu ya tsara kasafin ne a bisa hasashen farashin gangar ɗanyen man fetur a kan dala 64.85.

Haka an yi hasashen sama da gangar ɗanyen man fetur miliyan 1.84 a kullum, sannan ya ayyana canjin dala a kan naira 1,400.

Ma’aikatun da suka fi samun kasafi su ne Ma’aikatar Tsaro, inda za ta sami Naira tiriliyan 5.41, sai ababen more rayu, inda za a kashe Naira tiriliyan 3.56, yayin da Ma’aikatar Ilimi za ta kaishe Naira Tiriliyan 3.52, sai Ma’aikatar Lafiya kuma za ta kashe  Naira tiriliyan 2.48.

Tinubu ya ce tsaro shi ne ginshiƙin ci gaba, inda ya sanar da sake fasalin tsarin tsaron ƙasa da kuma sabon tsarin yaƙi da ta’addanci.

A fannin ilimi kuwa, Shugaban ya bayyana faɗaɗa Shirin Lamunin Ilimi na Ƙasa (NELFUND), wanda ya tallafa wa sama da dalibai 788,000 a manyan makarantu 229.

Yayin gabatar da Dokar Kasafin Kuɗi, Tinubu ya nemi haɗin kai tsakanin ɓangaren zartarwa da majalisa, yana mai cewa “Da haɗin kai da jajircewar al’ummar Najeriya, za mu cika dukkan alkawarin Ajandar Sabunta kudurori (Renewed Hope Agenda),” in ji shi.

Labarai

Labarai19 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai19 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai19 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai19 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai20 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara