Connect with us

Labarai

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Published

on

Daga Bello Wakili

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN, wanda ake sa ran Majalisar Dattijai za ta tabbatar da shi.

Nominaciyar tana bisa tanadin Sashe na 8, sakin layi na 1 na Dokar Central Bank of Nigeria Act 2007.

Nadin Yuguda ya biyo bayan nadin tsohon Mataimakin Gwamnan, Bala Bello, a matsayin Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Tattalin Arziki.

Shugaba Tinubu ya bukaci Yuguda da sauran jami’an bankin da su gudanar da ayyukansu bisa jajircewa, ƙwarewa, da sadaukarwa, domin tabbatar da daidaiton tattalin arziki da ci gaban kasa.

Lamido Yuguda ya taba rike mukamin slShugaban Hukumar Kasuwannin Hannun Jari daga shekarar 2020 zuwa 2024.

Ya samu digiri na farko a fannin Lissafi na Kasuwanci (Accountancy) aa Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya  a shekarar 1983, sannan daga baya ya samu digiri na biyu a fannin Kudi, wato Banking and Finance daga Jami’ar Birmingham a shekarar 1991.

Yuguda memba ne a Cibiyar Ƙwararrun Masu Lissafi ta Najeriya (ICAN)  kuma Ƙwararren Masanin Kudi.

Ya fara aikinsa a CBN a shekarar 1984 a matsayin Babban Mai Kula da Ayyuka a Sashen Harkokin Kudi na kasashen Waje.

Daga baya ya yi aiki a matsayin masanin tattalin arziki a sashen Afrika a Asusun Bada Lamuni na Duniya daga shekarar 1997 zuwa 2001 kafin ya koma CBN.

Ya yi ritaya daga CBN a shekarar 2016 bayan ya shugabanci Sashen Gudanar da Ajiyar Kudi na tsawon shekaru shida.

Labarai

Labarai18 hours ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai19 hours ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai20 hours ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai2 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai3 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi3 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai3 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai3 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Mafi Shahara