Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Bayyana Farin Cikinsa Bisa Sake Farfado Da Matatar Mai Ta Warri

Published

on

 

Shugaban kasa Bola  Tinubu ya bayyana matukar farin cikinsa kan sake bude matatar mai ta Warri (WRPC) da Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya yi, yana mai bayyana hakan a matsayin wata gagarumar nasara a shekarar 2024 wanda hakan ke kara wa ‘yan Najeriya kwarin gwiwa game da gwamnatinsa.

Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, ya sanar da cewa matatar mai ta Warri ta ci gava da aiki, makonni kadan bayan kamfanin NNPC ya  fara aikin  ganga 60,000 ta danya mai a kowace rana,a matatar mai ta Fatakwal, a watan Nuwamba.

Yayin da matatar ta Warri ta dawo aiki bayan shekaru da dama, shugaba Tinubu ya nanata kudurin gwamnatinsa na bunkasa aikin tace danyen mai da ake samu a gida Najeriya, da kuma sanya kasar a matsayin wata cibiya ta ayyukan masana’antu a Afirka.

Shugaban ya bayyana cewa tun farko gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari karkashin jam’iyyar APC ta bada kwangilar gyara matatun man kasar guda hudu.

Da yake magana game da wannan nasara, shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa karfin matatar mai ta Warri mai karfin 125,000 bpd, wanda a halin yanzu yana aiki da kashi 60 cikin 100, ya nuna gagarumin ci gaba a cikin shirin gwamnatinsa na tabbatar da ingancin makamashi da tsaro.

Shugaban ya yabawa shugaban kamfanin NNPCL Mele Kyari da tawagarsa, bisa jajircewar da suka yi na maido da martabar Najeriya a matsayin babbar kasa mai arzikin man fetur da kuma mayar da ita cibiyar tace danyen mai a Afirka.

Shugaba Tinubu ya kuma bukaci kamfanin NNPC da ya gaggauta aikin gyara matatar mai ta Kaduna da matatar mai mai karfin bpd 150,000 a Fatakwal, domin karfafa matsayin Najeriya a matsayin mai samar da makamashi a duniya.

Matatar mai ta Warri za ta mayar da hankali ne wajen samarwa da adana muhimman kayayyaki da suka hada daKalanzir, da iskar gas na mota, da sinadarin Naphtha, wanda zai kara habaka makamashin Najeriya da ayyukan masana’antu.

Daga Bello Wakili

Labarai

Labarai11 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi11 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai11 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara