Labarai
Shugaba Tinubu Ya Bayyana Farin Cikinsa Bisa Sake Farfado Da Matatar Mai Ta Warri
Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana matukar farin cikinsa kan sake bude matatar mai ta Warri (WRPC) da Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya yi, yana mai bayyana hakan a matsayin wata gagarumar nasara a shekarar 2024 wanda hakan ke kara wa ‘yan Najeriya kwarin gwiwa game da gwamnatinsa.
Bayo Onanuga, mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai, ya sanar da cewa matatar mai ta Warri ta ci gava da aiki, makonni kadan bayan kamfanin NNPC ya fara aikin ganga 60,000 ta danya mai a kowace rana,a matatar mai ta Fatakwal, a watan Nuwamba.
Yayin da matatar ta Warri ta dawo aiki bayan shekaru da dama, shugaba Tinubu ya nanata kudurin gwamnatinsa na bunkasa aikin tace danyen mai da ake samu a gida Najeriya, da kuma sanya kasar a matsayin wata cibiya ta ayyukan masana’antu a Afirka.
Shugaban ya bayyana cewa tun farko gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari karkashin jam’iyyar APC ta bada kwangilar gyara matatun man kasar guda hudu.
Da yake magana game da wannan nasara, shugaba Tinubu ya bayyana kwarin gwiwar cewa karfin matatar mai ta Warri mai karfin 125,000 bpd, wanda a halin yanzu yana aiki da kashi 60 cikin 100, ya nuna gagarumin ci gaba a cikin shirin gwamnatinsa na tabbatar da ingancin makamashi da tsaro.
Shugaban ya yabawa shugaban kamfanin NNPCL Mele Kyari da tawagarsa, bisa jajircewar da suka yi na maido da martabar Najeriya a matsayin babbar kasa mai arzikin man fetur da kuma mayar da ita cibiyar tace danyen mai a Afirka.
Shugaba Tinubu ya kuma bukaci kamfanin NNPC da ya gaggauta aikin gyara matatar mai ta Kaduna da matatar mai mai karfin bpd 150,000 a Fatakwal, domin karfafa matsayin Najeriya a matsayin mai samar da makamashi a duniya.
Matatar mai ta Warri za ta mayar da hankali ne wajen samarwa da adana muhimman kayayyaki da suka hada daKalanzir, da iskar gas na mota, da sinadarin Naphtha, wanda zai kara habaka makamashin Najeriya da ayyukan masana’antu.
Daga Bello Wakili
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
