Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu Ya Bukaci’Yan Majalisa Su Tsagaita Gayyatar Shugabannin Ma’aikatu

Published

on

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya roƙi ’yan Majalisar Wakilai da su daina yawan yi wa ministoci da shugabannin hukumomin Gwamnatin Tarayya kiranye da titsiye su kan ayyukan da suke gudanarwa.

Tinubu ya yi wannan roƙo ne yayin jawabinsa a wurin buda bakin da aka shirya wa ’yan Majalisar Wakilan ranar Laraba a Abuja.

Shugaban ya ce duk da cewa sa ido yana da matukar muhimmanci wajen tabbatar da gaskiya da riƙon amana a harkokin mulki, gayyato jami’ai fiye da kima na iya firgitasu ya kuma kawo cikas a tasirin ayyukan da za a yi wa ‘yan Najeriya.

Ya bukaci ‘yan majalisar da su nuna kwarewa wurin gudanar da ayyukansu na sa ido.

“Ina ganin yadda kwamitoci daban-daban su ke kiran ministoci da shugabannin hukumomi. Na kai kuka ga Shugaban Majalisa da cewa a bar talaka ya sarara.

“A bari mutanen nan su yi aikinsu. Ba ina cewa ba ku da tasiri ba ne, ba kuma ina cewa ku daina sa ido akan ayyukan da ake yi a ma’aikatu ba ne, roƙon da nake yi shi ne, ku barsu su yi aiki.

“Amma ku yi la’akari da aikin da kowace hukuma da ma’aikatanta ke yi. Kamar ayyukan da ke kan Gwamnan Babban Bankin ko kuma Ministan Tattalin Arziki na Kasa da Kudi da sauran al’umma baki ɗaya.

“Idan hankalinsu ya zama ba a kwance ba ko kuma suna kidime, to abubuwan ba za su tafi yadda kowa ke so ba, watakila sai kun fara zaman majalisa har cikin dare.

“Dole ne mu nemo hanyar da za mu zaunar da juna. Wannan roƙo ne gare ku. Ku duba yiwuwar amincewa da wakilan shugabannin ma’aikatu da ministoci a wasu lokuta ko ma takardu.”

Shugaba Tinubu ya bayyana jin dadinsa dangane da yadda Majalisar Dokokin ke ayyukanta.

Ya kuma jaddada godiya da jin daɗinsa akan yadda ake samun jituwa tsakanin bangaren zartarwa da Majlisar dokoki.

Ya ce, kyakkyawar alaƙar da ke tsakani ta ba majalisar damar amincewa da kudurorin bangaren zartarwa da a yanzu ‘yan Najeriya ke mora.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara