Connect with us

Labarai

An Mayar Da Gaza Maƙabarta Mafi Girma A Duniya — EU

Published

on

Babban jami’in kula da harkokin waje na Tarayyar Turai (EU), Josep Borrell  ya bayyana cewa, yaƙin da sojojin Isra’ila ke yi a Gaza ya mayar da yankin ya zama maƙabarta mafi girma a duniya.

“Gaza ta kasance tana da babban gidan yari mafi girma kafin fara yaƙin. A yau ita ce maƙabarta mafi girma a duniya, “in ji Borrell a taron ministocin EU a Brussels.

“Wata maƙabarta ce ga dubun dubatar mutane da kuma maƙabarta ga yawancin muhimman ƙa’idojin dokar jin ƙai.”

Borrell ya kuma sake nanata zarginsa da cewa Isra’ila na amfani da yunwa a matsayin “makamin yaƙi” ta hanyar ƙin barin manyan motocin agaji shiga Gaza.

“Isra’ila na amfani da matakin haifar da yunwa,” in ji shi a wani taron jin ƙai.

Ministan Harkokin Wajen Isra’ila, Isra’ila Katz, ya mayar wa Borrell martani, ya kuma ce masa da ya daina kai wa Isra’ila hari, mu kuma amince da ‘yancinmu na kare kai daga laifukan Hamas.

“Isra’ila ta ba da damar kai agajin jin ƙai mai yawa zuwa Gaza ta ƙasa, da sama da ruwa ga duk wanda ke son taimakawa,” in ji Katz kamar yadda ya bayyana kafar sadarwar zamani X (twitter).

Yaƙin Gaza mafi muni da aka taɓa yi ya ɓarke bayan da Ƙungiyar Hamas ta ƙaddamar da wani harin da ba a taɓa ganin irinsa ba, a ranar 7 ga watan Oktoba wanda ya yi sanadin mutuwar mutane kusan 1,160 a Isra’ila, galibi fararen hula, a cewar ƙididdigar da Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ya bayar bisa alƙaluman hukumomin Isra’ila.

Labarai

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai5 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara