Labarai
Majalisa ta amince ta ƙudurin sabon albashi ga alƙalan Najeriya
A ranar Laraba ne majalisar wakilai ta amince da ƙudirin dokar neman ƙarin albashi da alawus-alawus ga alƙalan Najeriya.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa Majalisar kudirin dokar domin tantancewa tare da amincewa da shi a ranar Talata.
Ƙudirin da aka amince da shi ya bayar da albashin jimlar naira miliyan 5.3 a kowane wata ga alƙalin alƙalai na Najeriya (CJN).
Ƙudirin ya kuma ce sauran alkalan Kotun Koli za su samu albashin naira 4.2 yayin da Shugaban Kotun ɗaukaka ƙara zai rika samun albashin naira miliyan 4.4 duk wata.
Haka kuma, alƙalan kotun ɗaukaka ƙara za su rika karɓar albashin naira miliyan 3.7 duk wata, yayin da ƙaramin alƙali zai karɓi albashin naira miliyan 3.5 duk wata.
A cewar ƙudirin, albashin na wata-wata ya kunshi cikakken albashinsu ne da duk wani alawus-alawus na yau da kullum da suka haɗa da samar da mai da kuma kula da ababen hawa da dai sauransu.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi6 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha6 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai6 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar