Connect with us

Fasaha

Sanƙarau Ta Kashe Mutum 6 A Gombe

Published

on

Akalla mutum shida ne suka rasu sakamakon kamuwa da cutar sanƙarau a Kananan Hukumomin Nafada da Funakaye a Jihar Gombe.

Kwamishinan Lafiya na jihar, Dokta Habu Dahiru ne, ya sanar da haka da yammacin ranar Alhamis.

 

Ya ce hukumar lafiya ta jihar ta gudanar da bincike tare da tabbatar da bullar cutar a kananan hukumomin biyu.

Ya ce an tabbatar da mutuwar mutum shida; mutum biyar a Karamar Hukumar Nafada, yayin da wani mutum daya ya rasu a Karamar Hukumar Funakaye.

A cewarsa sun samu rahoton bullar cutar ne a ranar 18 ga watan Fabrairu 2024, bayan yi es mutum 95 gwajin cutar a Babban Asibitin Garin Funakaye.

A cewar Kwamishinan, an sallami mutum 84 daga cikin mutum 95 da suka kamu da cutar, yayin da mutum shida ke ci gaba da karbar magani a asibiti.

Ya kara da cewar daga cikin wasu mutum 29 da aka yi gwaji, an samu mutum biyu dauke da cutar.

Gwamnan jihar, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayar da umarnin bayar da magunguna da tallafi ga asibitin don domin dakile yaduwar cutar.

Gwamnan ya umarci farfado da Cibiyar Dakile Cututtuka Masu Yaduwa (NCDC) a jihar.

Ya yi kira ga jama’ar jihar da kaucewa kwanciya cikin zafi da kuma cunkoso domin hakan na iya haifar da cutar sanƙarau.

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara