Nishadi
Murja Ta Kai Ƙarar Hisbah Gaban Kotu

Fitacciyar jarumar nan ta dandalin TikTok, Murja Ibrahim Kunya, ta yi ƙarar Gwamnatin Kano a gaban Babbar Kotun jihar.
Wannan dai na cikin ƙunshin takardar ƙarar da Murja ta shigar bisa wakilcin lauyoyinta — A. U Hajji da S.S Shehu — mai ɗauke da kwanan watan 26 ga Fabarairun 2024.
A ƙunshin ƙarar da Magatakardan Kotun, Adam S. Adam ya rattaba hatimi da kuma sa hannu, Murja ta buƙaci a shiga tsakaninta da Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Kwana Huɗu.
Aminiya ta ruwaito cewa, cikin jerin waɗanda ƙarar da Murja ta shigar ta shafa akwai Antoni-Janar na Jihar Kano da Kwamishinan ’Yan Sandan Kano, da Hukumar Hisbah da Hukumar Asibitocin Kano da Babban Asibitin Masu Larurar Kwakwalwa da ke Dawanau.
Takardar ta nuna cewa, Babbar Kotun ta cimma muradu huɗu daga cikin jerin buƙatu bakwai da lauyoyin Murja suka gabatar wa Mai Shari’a Nasiru Saminu.
Sai dai Aminiya ta lura cewa, daga cikin buƙatun lauyoyin Murja da kotun ta yi watsi da su, har da ta neman mayar wa wadda suke wakilta wayarta ta hannu kirar iPhone da kuma katin banki na ATM.
Da wannan hukuncin ne kotun ta kuma ɗage ƙarar zuwa 20 ga watan Maris na 2024.
Ana iya tuna cewa, a bayan nan dai Mai Shari’a Malam Nura Yusuf Ahmad na Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kwana Huɗu ya bayar da umarnin a yi wa Murja gwajin kwakwalwa.
Alkalin ya ba da umarnin ne bisa zargin jarumar ba ta cikin hayyacinta a lokacin zaman kotun na farko da aka gurfanar da ita.
Tun farko dai Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ce ta gurfanar da Murja kan zargin tayar da hankalin jama’a, bata tarbiyya da kuma koyar da karuwanci.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai6 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai5 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
