Connect with us

Ilimi

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Ba da Umarnin Rufe Makarantu 47 Nan Take

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta bada umarnin rufe makarantu arba’in da daya  saboda matsalolin tsaro.

A wata takardar sanarwa da aka aikewa dukkan Shugabannin makarantu, wadda Daraktan Makarantu Manyan Sakandare na Ma’aikatar Ilimi ya sanya wa hannu, gwamnati ta bayyana cewa sakamakon ƙalubalen tsaro da ake fuskanta a wasu sassan ƙasar nan da kuma buƙatar kare duk wani yunkurin hari, Ministan Ilimi ya amince a rufe makarantun nan dltaje.

Ga jerin makarantu da abin ya shafa:

  1. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Minjibir, Jihar Kano
  2. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Ganduje, Jihar Kano
  3. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Zariya, Jihar Kaduna
  4. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Kafanchan, Jihar Kaduna
  5. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Bakori.
  6. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Dayi, Jihar Katsina
  7. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Daura, Jihar Katsina
  8. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Tambuwal, Jihar Sakkwato
  9. Kwalejin Kimiyya ta Tarayya, Jihar Sakkwato
  10. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Wurno, Jihar Sakkwato
  11. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Gusau, Jihar Zamfara
  12. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Anka, Jihar Zamfara
  13. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Gwandu, Jihar Kebbi
  14. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Birnin Yari, Jihar Kebbi
  15. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Zuru, Jihar Kebbi
  16. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Kazaure, Jihar Jigawa
  17. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Kiyawa, Jihar Jigawa
  18. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Hadejia, Jihar Jigawa
  19. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Bida, Jihar Neja
  20. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, New Bussa, Jihar Neja
  21. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Kuta-Shiroro, Jihar Neja
  22. Akademiyar Gwamnatin Tarayya, Suleja, Jihar Neja
  23. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Ilorin, Jihar Kwara
  24. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Omu-Aran, Jihar Kwara
  25. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Gwanara, Jihar Kwara
  26. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Ugwolawo, Jihar Kogi
  27. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Kabba, Jihar Kogi
  28. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Ogugu, Jihar Kogi
  29. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Bwari, Abuja
  30. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Rubochi, Abuja
  31. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Abaji, Abuja
  32. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Potiskum, Jihar Yobe
  33. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Buni-Yadi, Jihar Yobe
  34. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Gashua, Jihar Yobe
  35. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Michika, Jihar Adamawa
  36. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Ganye, Jihar Adamawa
  37. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Azare, Jihar Bauchi
  38. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Misau, Jihar Bauchi
  39. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Bajoga, Jihar Gombe
  40. Kwalejin Gwamnatin Tarayya, Billiri, Jihar Gombe
  41. Kwalejin Fasaha ta Tarayya, Zambuk Jihar Gombe.
  42. Kwalejin ’Yan Mata ta Gwamnatin Tarayya, Bwari, Abuja.
  43. Kwalejin Fasaha ta Tarayya Ikare Akoko.
  44. Kwalejin Fasaha ta Tarayya Ijebu-Imusin.
  45. Kwalejin Fasaha ta Tarayya Ushi Ekiti.
  46. Kwalejin Gwamnatin Tarayya Ganye
  47. Kwalejin Gwamnatin Tarayya Billiri

Takardar ta umarci Shugabannin makarantu da abin ya shafa su tabbatar da cikakken bin wannan umarni.

 

RN

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara