Labarai
Gwamnan Kebbi Ya Bi Sahun Takwarorinsa Na Bada Tallafi Ga Alhazai
Gwamnatin jihar Kebbi ta amince da tallafin Naira miliyan daya ga kowane mahajjacin jihar su dubu uku da dari uku da arba’in da hudu domin sauke farali a aikin Hajjin shekarar 2024.
Kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Yakubu Ahmed Birnin Kebbi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai, biyo bayan taron gaggawa na majalisar zartarwar jihar da aka gudanar a ranar Litinin.
Ya ce, hakan ya biyo bayan karin kudin aikin Hajjin 2024 ne da Naira miliyan daya da dubu dari tara da Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta yi.
A cewar sa, za a biya Naira miliyan daya ga kowane maniyyaci da ya kammala biyan kudin aikin Hajjin sa a baya.
Dangane da batun fasa shaguna da sace-sacen hatsi da wasu baragurbi suka yi a babban birnin jihar, Kwamishinan ya ce, gwamnatin jihar ta yi Allahwadai game da hakan.
Alhaji Yakubu BK ya ce gwamnatin jihar ta yi tir da irin wadannan munanan dabi’u domin ba halayyar mutanen jihar ba ne.
Ya kara da cewa, an kafa kwamiti mai mutum 13 a karkashin jagorancin kwamishinan aikin gona don binciki lamarin.
Kwamitin, zai bankado musabbabin wannan aika-aikar, tare da tantance mutanen da ke da hannu tare da ba da shawarar hanyoyin hana sake aukuwar hakan.
Shima da yake magana akan lamarin, kwamishinan noma da albarkatun kasa, Alhaji Shehu Muazu, ya shaidawa manema labarai cewa, kayan agajin da aka wawashe na gidauniyar Dangote ce ba na gwamnatin jihar ba.
Abdullahi Tukur
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
