Connect with us

Kasuwanci

Gwamnan Kabawa Ya Tabbatarwa Ma’aikatan Gwamnati Ingantacciyar Walwala

Published

on

Gwamnatin jihar Kebbi, ta baiwa ma’aikatan jihar tabbacin ci gaba da jajircewa wajen kyautata jin dadin su da kuma kare hakkokinsu.

 

Gwamna Nasir Idris wanda ya ba da wannan tabbacin a lokacin da yake jawabi ga ma’aikata domin bikin ranar watan Mayu a Birnin Kebbi, ya jaddada cewa ma’aikata aminai ne masu kima wajen ci gaban jihar Kebbi, kuma su kasance masu ruwa da tsaki da ba za a yi watsi da su ba.

 

Gwamna Idris, wanda ya bayyana bikin ranar Mayu a matsayin wani muhimmin lokaci, ya yabawa ma’aikatan bisa jajircewarsu da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa wajen ci gaban jihar.

 

“Kwazonku da jajircewarku sune kashin bayan tattalin arzikinmu. Ina yaba muku kan kokarinku na jajircewa”.

 

Gwamna Idris, ya kuma amince da kalubalen da ma’aikatan jihar ke fuskanta tare da ba su tabbacin gwamnatinsa ta kudiri aniyar magance wadannan matsalolin.

 

A yayin da yake taya kungiyar kwadago ta Najeriya NLC da TUC murnar zagayowar ranar ma’aikata, Gwamna Idris ya nuna jin dadinsa ga kungiyar ‘yan kasuwa bisa jajircewar da suke yi na kyautata jin dadin ma’aikata sannan ya bukaci ma’aikata da su ci gaba da jajircewa wajen gudanar da ayyukansu tare da ci gaba da ciyar da jihar gaba.

 

Tun da farko a nasa jawabin, shugaban kungiyar kwadago ta kasa (NLC) na jihar, Kwamared Murtala Usman, ya bayyana jin dadinsa a madadin kungiyoyin NLC da TUC bisa yadda Gwamnan ya ba da kulawar da yake yi wajen kyautata jin dadin ma’aikata da ci gaban su.

 

Kwamared Usman ya yaba da irin goyon bayan da Gwamnan ke ci gaba da baiwa ma’aikata, inda ya bayyana halartan taron bikin ranar Mayun 2025 kamar yadda aka zata duba da tarihinsa a matsayinsa na tsohon dan kungiyar kwadago da kuma tsohon shugaban kwadago.

 

Muhimman abubuwan da suka wakana a wajen taron sun hada da fareti da ma’aikata suka yi, da bayar da lambar yabo ga gwamna Idris da kungiyar dalibai ta kasa (NANS) reshen jihar Kebbi da kungiyar ma’aikatan jinya ta kasa suka yi.

 

Shugabannin kungiyar NLC na jihar sun kuma mika kyautuka ga wasu fitattun mutane bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban jihar Kebbi.

 

COV/ Abdullahi Tukur

Labarai

Labarai5 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara