Labarai
An Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Na Jihohi Su Kafa Ma’aikatun Harkokin Iyali
An yi kira ga Gwamnatin tarayya da na jihohi da su kafa Ma’aikatu na Harkokin Iyali domin magance aikata laifuka da rushewar tarbiyya a ƙasar nan, wanda ake dangantawa da lalacewar abi’un iyali.
Limamin Masallacin Juma’a na Kofar Marusa da ke Katsina, Sheikh Nura Gwanda, ne ya yi wannan kira a cikin hudubar Juma’ar da ya gabatar mai taken “Iyaye da Tarbiyya a Matsayin Amanar Allah”.
Ya bayyana wasu daga cikin munanan dabi’u da suka bulla sakamakon rugujewar darajar iyali, da suka haɗa da shan miyagun ƙwayoyi, ta’addanci, fashi da makami, ‘yan daba, garkuwa da mutane da kuma rashawa a gwamnati da ma kamfanoni masu zaman kansu.
Sheikh Gwanda ya bayyana cewa mafi yawan ƙasashen Gabas ta Tsakiya da Turai suna da Ma’aikatu na Harkokin Iyali waɗanda ke kula da al’amurran aure, tarbiyyar yara, gado, cin zarafin iyali, cin zarafin yara, saki, kula da yara bayan rabuwar aure da sauran batutuwan iyali.
Ya jaddada cewa tunda iyali ne tubalin gina al’umma, kafa irin wannan ma’aikata a Najeriya zai taimaka matuƙa wajen shawo kan matsaloli irin su cin zarafin yara, zaman kashe wando, tabarbarewar tarbiyya da sauran munanan dabi’u musamman a arewacin ƙasar.
Liman ya ƙara da cewa kafa Ma’aikatar Harkokin Iyali zai kuma magance tushen matsalolin tsaro a ƙasar nan, duba da cewa mafi yawan masu aikata laifuka yara ne da aka yar da su ko kuma ‘ya’yan da iyayen su ba sa tare da juna.
Daga Isma’il Adamu
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
