Connect with us

Labarai

An Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Na Jihohi Su Kafa Ma’aikatun Harkokin Iyali

Published

on

An yi kira ga Gwamnatin tarayya da na jihohi da su kafa Ma’aikatu na Harkokin Iyali domin magance aikata laifuka da rushewar tarbiyya a ƙasar nan, wanda ake dangantawa da lalacewar abi’un iyali.

Limamin Masallacin Juma’a na Kofar Marusa da ke Katsina, Sheikh Nura Gwanda, ne ya yi wannan kira a cikin hudubar Juma’ar da ya gabatar mai taken “Iyaye da Tarbiyya a Matsayin Amanar Allah”.

Ya bayyana wasu daga cikin munanan dabi’u da suka bulla sakamakon rugujewar darajar iyali, da suka haɗa da shan miyagun ƙwayoyi, ta’addanci, fashi da makami, ‘yan daba, garkuwa da mutane da kuma rashawa a gwamnati da ma kamfanoni masu zaman kansu.

Sheikh Gwanda ya bayyana cewa mafi yawan ƙasashen Gabas ta Tsakiya da Turai suna da Ma’aikatu na Harkokin Iyali waɗanda ke kula da al’amurran aure, tarbiyyar yara, gado, cin zarafin iyali, cin zarafin yara, saki, kula da yara bayan rabuwar aure da sauran batutuwan iyali.

Ya jaddada cewa tunda iyali  ne tubalin gina al’umma, kafa irin wannan ma’aikata a Najeriya zai taimaka matuƙa wajen shawo kan matsaloli irin su cin zarafin yara, zaman kashe wando, tabarbarewar tarbiyya da sauran munanan dabi’u musamman a arewacin ƙasar.

Liman ya ƙara da cewa kafa Ma’aikatar Harkokin Iyali zai kuma magance tushen matsalolin tsaro a ƙasar nan, duba da cewa mafi yawan masu aikata laifuka yara ne da aka yar da su ko kuma ‘ya’yan da iyayen su ba sa tare da juna.

Daga Isma’il Adamu

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara