Connect with us

Labarai

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Published

on

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin kasancewa dalibin jami’ar yana aikata damfara ta yanar gizo tare da yin amfani da sunan wani.

A wata sanarwa da Daraktan Harkokin Hulɗa da Jama’a na jami’ar, Lamara Garba, ya fitar, jami’ar ta jaddada cewa tana da tsauraran ƙa’idoji kan halayya, ladabi da kuma ɗabi’ar da ake bukata daga dukkan dalibanta.

Jami’ar ta kuma bayyana cewa duk wani abu da wani dalibi ya aikata ba lallai ba ne ya wakilci dabi’u da martabar jami’ar gaba ɗaya.

Sanarwar ta ce bayan bullar zargin, jami’ar ta fara bincike na farko domin gano gaskiyar lamarin, inda hukumomin jami’ar ke duba batun bisa ƙa’idojin gudanarwa da hanyoyin ladabtarwa da aka tanada.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya bayyana ne bayan Farfesa Farooq Kperogi, malamin sadarwa ta zamani a wata jami’a da ke Amurka, ya bayyana a fili cewa wani da ake zargi da damfara yana ikirarin dalibi ne na BUK yana neman taimakon kuɗi tsawon shekaru domin biyan kuɗin makaranta.

Malamin ya gano cewa mutumin yana amfani da sunan ƙarya ne, har ma yana kwaikwayon mace domin samun kuɗi. Bayan wallafar bayanin Farfesa Kperogi, wasu mutane ma sun fito suna cewa su ma sun fuskanci irin wannan damfara.

Jami’ar ta yaba da ƙoƙarin Farfesa Kperogi da sauran mutane masu taimaka wa dalibai mabukata ta hanyar tallafa musu da kuɗin rajista da sauran bukatun karatu, tana mai cewa irin wannan taimako na taimakawa wajen faɗaɗa damar samun ilimi.

Jami’ar ta kuma tabbatar wa jama’a cewa idan bincike ya tabbatar da zargin, za a ɗauki matakin ladabtarwa da ya dace bisa dokokin jami’ar da kuma dokokin ƙasa.

Har ila yau, jami’ar ta bukaci jama’a da su bar binciken ya kammala cikin natsuwa tare da kauce wa yaɗa bayanan da ba a tabbatar da sahihancinsu ba.

Rel / Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai2 hours ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai3 hours ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai3 hours ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai3 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai3 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara