Connect with us

Kasuwanci

Daliban BUK 300 Za Su Ci Gajiyar Horon Aikin Gona don Kasuwanci

Published

on

Cibiyar Noma a Yankunan Busassu (Centre for Dryland Agriculture – CDA) ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta haɗa gwiwa da Ƙungiyar Ci Gaban Mata Manoma (Women Farmers Advancement Network – WOFAN) da kuma Kwalejin Aikin Gona, domin horas da daliban aikin gona 300 a duk shekara kan harkokin noma don kasuwanci da ƙara darajar amfanin gona, sarrafawa da kuma samarwa, ƙarƙashin shirin SIBLING Project.

Shirin, wanda ya shafi daliban matakai na aji 3 zuwa 4, an bayyana shi ne yayin wata ziyarar girmamawa da tawaga ta haɗin gwiwa daga WOFAN, CDA da Kwalejin Aikin Gona suka kai wa Shugaban Jami’ar, Farfesa Haruna Musa.

A ƙarƙashin shirin, CDA ta ware filin gwaji mai girman hekta biyu, yayin da Kwalejin Aikin Gona ta samar da hekta 25 domin noman manyan gonaki da horo na aikace-aikace.

Shirin zai kuma bai wa dalibai damar fahimtar darajar noma da kasuwancin noma da kwarewar aikace-aikace da ke taimakawa bunƙasa aiki mai ɗorewa.

Da yake jawabi a lokacin ziyarar, Farfesa Haruna Musa ya yaba da haɗin gwiwar, inda ya bayyana ta a matsayin muhimmin tsari na ƙarfafa matasa da mata, yana mai nuna cewa mata 180 ne daga cikin daliban 300 da za su amfana da shirin.

Da yake karin haske kan haɗin gwiwar, Daraktan CDA, Farfesa Sanusi Gaya Mohammed, ya bayyana cewa CDA da WOFAN sun samu damar amfani da rumbun ajiya na ƙasa ta hannun Cibiyar Ƙasa ta Inganta Ayyukan Rumbunan Ajiya ta Nijeriya (National Storage Productivity Institute of Nigeria).

A nata jawabin, Daraktar WOFAN a ƙasa, Dakta Salamatu Garba, ta ce shirin na da nufin sauya yadda mata da matasa ke shiga harkar noma ta hanyar basu kwarewa, samun filayen noma da kayan aiki, tare da kasuwa mai tabbas.

Shi ma yana jawabi, Dekan Kwalejin Aikin Gona, Farfesa Muhammad Auwal Hussain, ya ce shirin ya samo asali ne daga buƙatun dalibai da matan ma’aikata, tare da haɗa al’ummomi biyu daga yankin Zango domin ƙarfafa hulɗar al’umma da ci gaba mai haɗa kowa da kowa.

Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara