Connect with us

Ilimi

NELFUND Ya Raba Sama da Naira Biliyan 3 ga Daliban BUK

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Asusun Bada Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND) ya raba jimillar Naira Biliyan 3 da Miliyan 39 a matsayin kudaden karatu ga daliban Jami’ar Bayero da ke Kano su  27,640,  a wani  mataki na fadada damar samun ilimi cikin sauki.

Shugaban Jami’ar, Haruna Musa ne ya bayyana hakan yayin wata ziyarar girmamawa da Darakta Janar na NELFUND, Akintunde Sawyerr, tare da tawagarsa suka kai jami’ar.

Ziyarar, na da nufin karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu da kuma tattauna batutuwan da suka shafi kudaden da ke bai wa dalibai.

A jawabinsa, Farfesa Haruna Musa ya yaba wa NELFUND kan irin tasirinsa ga dalibai, yana mai cewa shirin ya taimaka matuka wajen kara damar shiga makarantu ga dimbin ‘yan Najeriya da ba za su iya yin rajista ba a baya.

Ya ce a zangon karatu na shekarar 2023/2024, daliba BUK 113 ne suka ci gajiyar shirin, inda aka biya Naira Biliyan 1 da Miliyan 494 a matsayin kudaden karatu.

Ya kara da cewa adadin ya karu sosai a zangon 2024/2025 zuwa dalibai 14,539, wanda kudaden suka kai jimillar Naira Biliyan 1 da Miliyan 545.

Gaba daya, jimillar dalibai 27,640 daga Jami’ar Bayero sun amfana da shirin NELFUND, inda kudaden makaranta suka kai Naira Biliyan 3 da Miliyan 39, baya ga kudaden amfanin yau da kullum da ake biya kai tsaye ga daliban,” in ji shi.

Sai dai Shugaban Jami’ar ya bayyana cewa wasu dalibai sun fuskanci matsaloli yayin neman lamunin da kuma karbar kudade ta shafin NELFUND. Inda ya bayyana fatan tawagar za ta zage damtse wajen tabbatar da magance wadannan matsaloli.

Tun da farko, Mista Sawyerr ya ce ziyarar na da nufin  kara zurfafa hadin gwiwa ne da jami’ar, yana mai tabbatar da cewa za a duba korafe-korafen dalibai domin saukaka tsarin neman lamunin da sake nema.

Haka kuma ya shawarci jami’ar da ta rika bude shafinta a kan lokaci domin bai wa dalibai damar yin rajista da wuri, tare da samun kudaden amfanin yau da kullum ba tare da jinkiri ba.

Labarai

Ilimi2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Wasu Sabbin Ka’idoji Kan Digirin Girmamawa

Daga Bello Wakili Gwamnatin Tarayya ta amince da wani sabon tsari game da bayar da digirin girmamawa (honorary degrees) a...

Labarai2 days ago

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar da Nadin Sabbin Ministoci Biyu

Daga Bashir Meyere  Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin ministoci biyu da Shugaban Ƙasa ya miƙa sunayensu domin tantance su...

Labarai2 days ago

Rukuni na Farko na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasar Saudiyya

Daga Ali Muhammad Rabi’u Rukuni na farko na Alhazan Jihar Kwara su 374 ya sauka ƙasar Saudiyya domin gudanar da...

Labarai2 days ago

Jihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki

Daga Usman Muhammad Zaria Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce rukuni na biyu kuma na ƙarshe na...

Labarai2 days ago

Gwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida

Daga Aliyu Lawal Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya jajanta wa al’ummar yankunan ƙananan hukumomin Bida da Mokwa kan...

Kasuwanci2 days ago

BOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu

Daga Salihu Tsibiri Bankin Manoma na Kasa (BOA) zai hada gwiwa da Majalisar Wakilai ta Tarayya domin bunkasa amfani da...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta Mayar da Rarar Kudade ga Alhazai

Daga Abdullahi Jalaluddeen Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta kammala biyan rarar kuɗaɗe ga maniyyata aikin Hajjin 2026....

Ilimi2 days ago

UNICEF Ta Ƙara Faɗaɗa Ayyukanta Domin Inganta Rayuwar Yara a Najeriya

Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF, ta ƙara faɗaɗa ayyukanta a faɗin Najeriya domin inganta...

Labarai4 days ago

Gwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya buƙaci Alhazan jihar da su kasance jakadu nagari yayin zamansu a ƙasa mai tsarki....

Mafi Shahara