Connect with us

Labarai

BUK Ta Shirya Taro Kan Inganta Harkokin Kudi A Aikin Gwamnati

Published

on

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta sake jaddada kudirinta na ci gaba da samar da sauye-sauyen zamani wajen tafiyar da  harkokin kuɗi a aikin gwamnati a Najeriya da sauran kasashen Afirka.

Shugaban jami’ar, Farfesa Haruna Musa ne ya bayyana wannan kudirin a taron ƙasa da ƙasa na farko kan harkokin mulkin jama’a, wanda sashen gudanarwa na jama’a, karkashin tsangayar nazarin harkokin tattalin arziki ta shirya.

Shugaban, wanda Mataimakiyar Shugaban Jami’a mai kula da Bincike da Cigaba, Farfesa Amina Mustapha ta wakilta, ya jaddada cewa BUK na kan gaba wajen jagorantar harkokin ilimi da suka dace da muradun ‘yan ƙasa bisa ƙa’idojin duniya.

Ya bayyana taken taron a matsayin abin da ya dace a wannan lokaci, tare da yin kira ga mahalarta da su yi amfani da ilimin da suka samu domin inganta tsarin mulki a Najeriya da Afirka.

A cikin saƙon fatan alheri, shugaban taron kuma Shugaban Hukumar Bincike da Cigaban Ilimin Najeriya (NERDC), Farfesa Salisu Shehu, ya jaddada canjin gaggawa da tattalin arzikin zamani ya haifar.

Ya ce Afirka na fuskantar sauye-sauye masu ban mamaki, kuma irin waɗannan taruka na zama tamkar ƙarfafa ingantaccen mulki da gaskiya ne a harkokin kudi.

Mai gabatar da muƙalar farko, Matawallen Zazzau kuma malami a Jami’ar Kaduna, wanda shi ne shugaban Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomin Jihar Kaduna, Farfesa Aminu Ladan Sharehu, ya bayyana hanyoyin da Afirka musamman Najeriya za ta iya sauya manufofin jama’a da tsarin kuɗi domin haɓaka cigaba mai ɗorewa.

Ya lura cewa taron ya mai da hankali ne wajen nazarin yadda za a iya amfani da manufofin jama’a da tsarin kuɗi wajen inganta mulki mai nagarta.

Ɗaya daga cikin mahalarta taron, Mataimakin Daraktan Gudanarwa na Ƙaramar Hukumar Sabon Garin Jihar Kaduna, Nura Ibrahim Aminu, ya bayyana muhimmancin shirye-shiryen da al’umma suka jagoranta da kuma tarurrukan tattaunawa a yankuna wajen inganta gaskiya da cigaban ƙasa daga tushe.

Taron, na yini uku, mai taken “Sauya Manufofin Jama’a, Harkokin Kuɗi da Gudanarwa Domin Cigaba mai Ɗorewa a Afirka: Matsaloli, Kalubale da Hanyoyin Magance Su” ya samu  mahalarta masana da dama daga ciki da wajen ƙasa.

 

Daga Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara