Labarai
NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka da ’yan bindiga a karamar hukumar Patigi.
A wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Ayoola Ishola, ya fitar, ya ce an kama Abubakar Jubril da Mohammed Abubakar ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai bisa bayanan sirri.
Sanarwar ta ce an hango mutane uku a wani yanki mai fama da matsalar tsaro, inda aka kama biyu daga cikinsu, yayin da daya ya tsere kuma ake ci gaba da nemansa.
An kuma kwato wasu kayayyaki daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da bindiga karama, wayar salula, da wasu kwayoyi da ake zargin Tramadol ne, da kuma taba sigari.
Da yake gabatar da wadanda ake zargin, kwamandan NSCDC a jihar, Bala Bodinga, ya ce hukumar za ta ci gaba da yaki da ayyukan ta’addanci domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya kuma gargadi masu aikata laifi su daina, tare da bukatar jama’a su rika bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaki da laifuka.
Ali Muhammad Rabi’u/Ilorin
-
Labarai6 days agoAna Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
-
Labarai7 days agoJam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano
-
Labarai5 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoGwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya
-
Labarai4 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai4 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Ilimi6 days agoGwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
