Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Published

on

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da mukamin wajen fa’ida ta kansa, da cin amanar jama’a.

Wannan mataki ya biyo bayan korafi da aka mika ga Majalisar daga Shugaban Gwamnati, inda aka bukaci majalisar ta dauki mataki kan Mataimakin Gwamnan saboda zargin rashin da’a a lokacin da yake kwamishinan Harkokin Kananan Hukumomi tsakanin shekarar 2023 zuwa 2024.

Jagoran masu rijaye a majalisar Lawan Hussaini Dala, ya ce sanarwar tsigewar ta dace da Sashe na 188 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya (1999, da aka gyara).

A cewarsa, sanarwar ta nuna cewa Abdulsalam ya aikata abubuwan da ke iya janyo tsige shi yayin da yake kula da kananan hukumomi 44 na jihar.

Zargin da korafin ya kunsa sun hada da: Cin amanar jama’a da Juyar da kudade da Yin amfani da mukami ba bisa ka’ida ba da kuma Rashin da’a da manyan laifuka

An ce:“Abdulsalam ya yi amfani da kudaden da aka ware domin kananan hukumomi domin amfanin kansa. Daga Yuni 2023 zuwa Janairu 2024, an ce ya karɓi ₦462 miliyan a matsayin ribar da aka biya shi. Daga Fabrairu 2024 zuwa Yuli 2024, an ce ya karɓi ₦726 miliyan daga kananan hukumomi ta hanyar aikin musamman.”

Haka kuma, an ce Abdulsalam ya ba da damar sakin ₦440 miliyan ga kamfanin North Med Pharmaceutical Limited ba bisa ka’ida ba, wanda ya saba dokokin sayen kaya na gwamnati da tsarin kasafin kudin jihar.

Dala ya bayyana cewa: “Wadannan ayyuka suna cikin manyan laifuka a ƙarƙashin Sashe 188(2) na Kundin Tsarin Mulki, kuma suna nuna karya ka’idojin mulki da dabi’un shugabanci.”

Dala ya kara da cewa, bisa ga hujjojin da aka gabatar, Abdulsalam ya kamata a korar sa daga mukami bisa tsarin doka.

Rahoton Radio Nigeria ya nuna cewa an bai wa Mataimakin Gwamnan makonni biyu domin ya mayar da martani kan zargin da ke cikin korafin.

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai4 hours ago

Ramadan: Tinubu Ya Kara Jaddada Kudirinsa na Inganta Rayuwar Jami’an Soji

Daga Bello Wakili  Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana godiya ga jami’an Rundunar Sojin Najeriya bisa sadaukarwar da suke...

Labarai4 hours ago

Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Harin Ta’addanci a Kauyen Ngoshe na Jihar Borno

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana alhinin sa tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda harin ta’addancin...

Labarai11 hours ago

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba ya kaddamar da sabbin...

Labarai11 hours ago

Tsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki

Majalisar Kasa Kan Abinci da Gina Jiki, wacce Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ke jagoranta, ta kafa wani kwamiti na...

Labarai11 hours ago

Hukuncin Kwamitin PAC kan Kudin NNPCL

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a ya kira tsofaffin shugabannin NNPCL da shugabannin yanzu domin su bayyana dalla-dalla kan hanyoyin...

Labarai11 hours ago

Kotun Kwara Ta Yanke Wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Ta Rataya

Babban Kotun Jihar Kwara dake Ilorin, karkashin jagorancin Alƙali Ahmed Aliyu Gegele, ta yanke wa mutane biyu hukuncin kisa ta...

Labarai11 hours ago

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam

Majalisar Dokokin Jihar Kano (KNHA) ta fara shari’ar tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam bayan tuhumar aikata manyan laifuka, amfani da...

Labarai11 hours ago

Uwargidan Gwamnan Jihar Kabi Ta Yaba Da Shirin Agajin Tukur Wasoso

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasare-Nasir, ta yi kira ga mutane masu arziki da su dauki darasi daga aikin...

Labarai11 hours ago

Sojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa

Sojojin Najeriya sun karɓi motocin Vanquisher Light Armoured Personnel Carriers da aka kera a cikin ƙasa daga kamfanin sarrafa makamai...

Labarai11 hours ago

FUGUS Za Ta Kafa Cibiyar Tarihi da Al’adu ta Zamfara

Shugaban Jami’ar Tarayya dake Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya bayyana shirin kafa Cibiyar Bincike da Rubuce-Rubuce kan Tarihi da...

Mafi Shahara